Kungiyar cigaban Matasan Arewa (AYCF) ta yi tir gami da Allah wadai da yin garkuwa da wasu ‘yan jarida biyu da iyalansu da ‘yan Ta’adda su kayi a Kaduna. A cikin wata takardar sanarwa da shugaban kungiyar na ?asa Alhaji Yerima Shettima ya fitar, ya bayyana sace ‘yan Jaridar a matsayin tsagwaron rashin imani sannan ya yi kiran sakin su cikin gaggawa ba tare da ?ata lokaci ba. Shettima ya ?ara da cewar labari ne mai tayar da hankali sace Alhaji Abdulghaffar Alabelewa na jaridar The Nation da matarsa da…
Read MoreCategory: Labaru
Labaru
An Sake Zaben Tinubu A Shugabancin ECOWAS Karo Na Biyu
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa, aby sake za?en shugaban kasa Bola Tinubu a matsayin shugaban ECOWAS karo na biyu cikin shekara guda. Sauran shugabannin ECOWAS, sun yanke shawarar sake za?arsa a taron ?ungiyar karo na 65 wanda ya gudana a fadar gwamnati da ke Abuja ranar Lahadi. Tinubu, cikin jawabinsa bayan sake za?arsa a matsayin shugaban ECOWAS, ya ce zai ci gaba da jan ragamar ?ungiyar domin kawo sauye-sauye masu alfanu. “Na amince na ci gaba da jan ragamar shugabancin wa?annan maza da mata…
Read MoreKaduna: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Shugaban Kungiyar ‘Yan Jarida Da Iyalansa
Rahotannin dake shigo mana daga Jihar Kaduna na bayyana cewa ‘yan ta’adda masu Garkuwa da mutane sunkai hari jiya asabar a unguwar Danhoni, dake cikin Karamar hukumar Chikun Jihar Kaduna Sunyi awon gaba da yan jaridu 2 da iyalansu. ‘yan jaridar sune Abdulgafar Alabelewe Na jaridar ( The Nation) da Abduraheem Aaodu na jaridar The Nation da (Blueprint) anyi Garkuwa da su a Daren Asabar a cikin gidajensu. Alabelewe shine shugaban kungiyar wakilan kafafen yada labarai na kasa reshen Jihar Kaduna, an sace shi ne tare da matarsa da yaransa…
Read MoreSama Da Kashi 64 Na ‘Yan Najeriya Za Su Fuskanci Barazanar Yunwa – Majalisar Dinkin Duniya
Majalisar Dinkin Duniya ta yi garga?in cewar ‘yan Najeriya miliyan 82 – kimanin kashi 64 na ‘yan ?asar – ka iya fuskantar matsalar yunwa nan da shekarar 2030. Haka kuma Majalisar ta yi kira da gwamnatin ?asar ta magance matsalar sauyin yanayi da matsalar ?wari da sauran abubuwan da yi wa harkar noma barazana. Jaridun Najeriya sun ambato jami’in Majalisar Dinkin Duniyar, Taofiq Braimoh – wanda ya wakilci kodinetan ayyukan jin ?ai na hukumar abinci da ayyukan noma na majalisar – na bayyana haka lokacin da yake jawabi kan matsalolar…
Read MoreYarjejeniyar SAMOA: Malaman Addini Sun Yi Tir Da Rattaba Hannun Gwamnatin Tarayya
Malaman addinin musulunci da-dama sun fito sun yi magana bayan jin labarin Najeriya ta shiga yarjejeniyar Samoa. Abin da ya jawo surutu da korafi shi ne ganin cewa akwai batun halatta aure da dangantakar jinsi a wannan yarjejeniya. A hudubobin da aka gabatar a garuruwa dabam-dabam, malaman addinin musulunci sun nuna ba za su goyi bayan alakar jinsi ba. Sheikh Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemu wanda malami ne a jami’a a hudubarsa ta Juma’a ya yi tir da yadda aka amince da yarjejeniyar. Shehin malamin ya ce bayan an shiga…
Read MoreBabu Batun Luwadi Da Madigo A Dokar Da Muka Sanya Wa Hannu – Fadar Shugaban Kasa
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa ministan ya?a labarai da wayar da kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ba za ta goyi bayan duk wani yun?uri na auren jinsi ko ?aure wa ‘yan luwa?i da masu ma?igo a Nijeriya ba. Ministan ya fa?i haka ne a yayin da yake martani kan labarin da aka ya?a a ranar Alhamis cewa Gwamnatin Tarayya ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya da aka yi a ?asar Samoa, wadda za ta ba da dama a…
Read MoreMajalisar Dattawa Ta Gano Shigowar Wani Gurbataccen Man Fetur Mai Hatsari A Najeriya
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa mjalisar Dattawan Najeriya ta ankarar da ‘yan ?asar cewa an shigo da wani nau’i na gur?ataccen man fetur da kuma dizel cikin ?asar. Da yake gabatar da wani ?udiri a ranar Laraba, Sanata Asuquo Ekpeyong ya ce a ranar 16 ga watan Yunin 2024 wani rahoto ya nuna cewa wasu jiragen dakon kaya 12 sun kai tan 660 na man dizel zuwa birnin Lome na Togo, inda daga nan aka rarraba su zuwa ?asashen Afirka ta Yamma musamman Najeriya.…
Read MoreAn Tsame Manoma Da Kananan ‘Yan Kasuwa Daga Harajin Cinikayya A Najeriya
Gwamnatin Najeriya ta tsame manoma da ?ananan ?an kasuwa da masu kamfanoni daga biyan haraji na cinikayya. Shugaban kwamitin shugaban ?asa kan yi wa haraji garambawul a Najeriya, Taiwo Oyedele ne ya sanar da matakin a shafinsa na X. Ya ce muhimman sauye-sauyen da aka yi za su magance matsalolin da aka gano da kuma sanya masu ?ananan sana’oi cikin wa?anda aka tsame daga biyan harajin cinikayya, tsame masu kamfanoni da masu sarrafa kayayyaki kamar manoma: matakan da za su magance kauce wa biyan haraji. Ya ce an bijiro da…
Read MoreDalilanmu Na Neman Bahasi A Wajen Sarkin Katsina – Gwamnatin Katsina
Gwamnan Jihar Katisna Mallam Dikko Umar Radda ya bu?aci Sarkin Katsina, Alhaji Abdulmumini Kabir Usman ya yi masa bayanin dalilin rashin halartar wasu hakiman masarautarsa bikin hawan sallah da aka gudanar a masarautar. Kwamishinan ya?a labarai da al’adun gargajiya na jihar, Dakta Bala Salisu Zango ya tabbatar wa BBC cewa ba wata gagarumar matsala aka samu tsakanin gwamna da sarkin ba, face kawai batu ne na neman bahasi kan gazawar wasu hakimai wajen halartar hawan sallah duk da shirin da aka yi tun farko. ”Gwamnanmu mutum ne mai sha’awar abubuwan…
Read MoreGwamnatinmu Ba Za Ta Lamunci Zubar Da Jinin ‘Yan Kasa Ba – Tinubu
Sugaban ?asa, Bola Tinubu ya yi allawadai da harin ?unar ba?in waken da ya kashe a?alla mutum 18 a garin Gwoza na jihar Borno. Shugaba Tinubu a cikin sanarwar da ya fitar a ranar Lahadi, ya ce harin babban abin tashin hankali. “Masu tayar da rikici su sani cewa za su fuskanci hukunci daidai da su, kuma wa?annan matsoratan da ke kai wa mutane hari, su sani cewa gwamnatinmu ba za ta zura ido ana zubar da jinin jama’a da kuma jefa su cikin tsoro da fargaba ba” inji sanarwar…
Read MoreYadda Malami Ya Yi Badda Bami Da Kudaden Da Muka Kwato Hannun Barayin Gwamnati – Shugaban Kwamitin Bincike
Tsohon shugaban kwamitin kwararru da aka kafa domin bincike da kwato kudin jama’a da aka sace, Okoi Obono-Obla ya fadi inda aka kai kudaden. Mista Obono-Obla ya yi ikirarin cewa dukkanin kudin da aka kwato a zamanin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari an mayar da su ga barayin kasar ne. Ya kara da cewa gwamnatin Buhari ta gaza a wajen yaki da cin hanci da rashawa, gwamnatin da ya ce al’ummar Najeriya suka dorawa yarda in ji rahoton Obono-Obla, wanda Buhari ya nada shi matsayin hadiminsa, ya yi wannan ikirarin…
Read MoreKallo Ya Koma Sama: Gwamna Abba Ya Sha Alwashin Kwato Naira Biliyan 5.6 Na ‘Yan Fansho Da Ake Zargin Ganduje Ya Sunkume
Wata sabuwar batarna?a ta kunko kai a Kano, yayin da Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir-Yusif ya sha alwashin ?wato ku?a?en fansho N5.4bn da gwamnatin tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje ba ta biya ba, amma kuma ta fitar da ku?a?en. Gwamna Abba Kabir-Yusuf na Jihar Kano ya ce a shirye ya ke ya yi amfani da duk wata hanya ta doka wajen kar?o ku?a?en fansho da Gwamnatin Abdullahi Ganduje ta ke cirewa duk wata daga albashin ma’aikata da suka kai sama da Naira biliyan 5 kuma ba a sanya su a…
Read MoreKwalara: Gwamnatin Tarayya Ta Shawarci ‘Yan Najeriya Su Kaurace Wa Shan Fura, Kunu Da Zobo
Labarin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa dngane da yaduwar cutar kwalara, gwamnatin tarayya ta bukaci ?an Najeriya da su guji shan abin sha na gida irin su kunu, zobo da fura domin gujewa ?arkewar cutar kwalara. Karamin Ministan Muhalli, Iziaq Salako ne ya bayar da shawarar a wata sanarwa da ya fitar a Abuja, a ranar Litinin. Salako ya hori ?an Najeriya da su ?auki matakan kariya kamar tsaftace muhallinsu a koda yaushe da zubar da shara yadda ya kamata a wuraren da aka kebe.
Read MoreJirgin Shugaban Kasa: Za A Sayo Wa Tinubu Tsohon Jirgin Da Bankin Jamus Ya Kwace Hannun Wani Balarabe Mai Taurin Bashi
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa Jaridar PREMIUM TIMES na da tabbacin cewa shi ma Jirgin Shugaban ?asa da ake ta ha?ilon sayo wa Shugaban ?asa Bola Tinubu, tsoho ne, kuma daga wani Bankin Jamus za a sayi jirgin, wanda Bankin Jamus ya ?wace daga hannun wani attajirin Balarabe mai taurin-bashi. Jirgin dai samfurin Airbus A330 ne da aka ?wace daga hannun Balaraben, wanda wani babban dillalin fetur ne da ya kasa biyan bankin wani bashin ma?udan ku?a?en da ya ke bin sa. Sai dai…
Read More‘Yan Bindiga Sun Yi Wasoson Mata Da Kananan Yara A Mahaifar Karamin Ministan Tsaro Bello Matawalle
Rahotannin dake shigo mana daga Gusau babban birnin Jihar Zamfara na bayyana cewa, wasu ‘yan bindiga sun kai hari tare da yin garkuwa da mutane 47 daga kauyen Danbaza a karamar hukumar Maradun mahaifar ?aramin ministan tsaro Bello Matawalle. Wani mazaunin ?auyen, Abdul Danbaza, ya bayyana cewa ?an bindigar sun mamaye garin da misalin ?arfe 2:30 na dare ranar Laraba. Ya shaidawa jaridar Leadership cewa maharan sun yi awon gaba da mutane 47 galibi mata da ?ananan yara zuwa cikin jeji. Abdul ya ce ?an bindigar, wa?anda adadinsu ya kai…
Read MoreNajeriya Za Ta Fara Jigilar Jan Nama Da Waken Suya Zuwa Saudiyya
Ministan Harkokin Noma na Nijeriya Mohammad Abubakar ya ce Saudiyya ta nuna sha’awar fara shigar da ton 200,000 na naman shanu da ton miliyan ?aya na waken suya cikin ?asarta duk shekara daga Nijeriya. Minista Mohammed ya shaida wa manema labarai a ranar Alhamis a Abuja cewa Saudiyya ta nuna sha’awar hakan ne bayan da Ministanta na Harkokin Noma ya ziyarci Nijeriya tare da yin wasu taruka da ‘yan kasuwa a fannonin noma. “Nuna sha’awar tasu kan wannan batu ke da wuya sai muka fitar da wani tsari da za…
Read MoreNajeriya Ba Ta Taba Yin Shugaba Mai Gaskiya Da Rikon Amana Kamar Tinubu Ba – Shettima
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya roki ‘yan Najeriya wurin kimanta gwamnatin Bola Tinubu a kasar. Shettima ya bukaci ‘yan kasar su yiwa Tinubu adalci yayin kimanta gwamnatinsa duba da kokarin da yake yi wurin daidaita kasar. Shettima ya bayyana haka ne a ran Juma’a 28 ga watan Yunin 2024 yayin wani babban taro a Abuja, Tsohon gwamnan Borno ya ce Tinubu na aiki ba dare ba rana domin ganin ya inganta kasa . Ya kuma ba da tabbacin…
Read MoreSiyasar 2027: El-Rufa’i Na Shirin Shiga Darikar Kwankwasiyya
Labarin dake shigo mana daga Jihar Kaduna na bayyana cewa jigon Jam’iyyar NNPP Mai kayan Marmari, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso, ya ziyarci tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El’rufai a gidan sa dake babban Birnin tarayya Abuja. Ana dai ganin ziyarar na da ala?a da El-Rufai na shirin barin APC zuwa NNPC dan takawa Tinubu Birke da kuma marama Rabiu Musa Kwankwaso baya dan za?en 2027 kamar yadda masu sharhi suka bayyana. Akwai tsohuwar alaka tsakanin Kwankwaso da El’rufai tun lokacin yana Ministan tsaro shi Kuma yayi Ministan Birnin…
Read MoreDa Sojoji Ake Hada Baki Wajen Satar Danyen Mai – IPMAN
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa babban Kodinetan ?ungiyar Manyan Dillalan Fetur na Najeriya (IPMAN), ya yi zargin cewa da ha?in bakin jami’an tsaron Najeriya ake ?ibga satar ?anyen mai a kasar nan, can a yankin Neja Delta. Ya bayyana haka a wata tattaunawa da shi da aka yi a gidan talabijin na Arise TV. Musa Saidu ya ce duk da irin hanyoyin da?ile yawan satar tulin ?anyen mai da NNPC ya shigo da su, amma abin ba?in ciki wasu jami’an tsaro na yi masu…
Read MoreSokoto: Kotu Ta Hana Tube Rawunnan Wasu Hakimai
Babbar kotu a jihar Sokoto ta dakatar da gwamnan jihar, Ahmed Aliyu daga tube rawanin biyu cikin hakimai 15 da gwamnatinsa ta tsige. Hakiman Tambuwal da Kebbe, Alhaji Buhari Tambual da Alhaji Abubakar Kassim, wadanda ke cikin hakiman da gwamnatin jihar ta tube ne suka shigar da karar. Gwamnatin ta dauki mataki a kan su ne bisa zargin hannu a matsalar tsaro da kuma kin yin biyayya. Alkalin kotun, mai shari’a Kabiru Ibrahim Ahmed ya bai wa gwamnan da alkalin alkalan jihar da fadar sarkin musulmi da su soke tubewar…
Read More