Hukumar nazari da binciken sararin samaniya na Kasar Amurka “National Aeronautics and Space Administration” (NASA) tace ranar Litinin 8-4-2020 ( nan da kwanaki biyu) duniyarmu na Earth zata fuskanci mafi tsananin zazzabin Rana (Sun Eclipse) Kamar yadda sakamakon binciken NASA ya nuna, duk bayan shekaru 364 duniyar mu tana samun irin wannan zazzabi mafi girma da tasiri da yake jikkata Rana Mutanen duniya da suka rayu shekaru 364 da ya wuce sunga irin zazzabin, to bayan anyi wannan na ranar Litinin idan Allah Ya kaimu ba za’a sake fuskantar zazzabin…
Read MoreCategory: Tsarin Rayuwa
Tsarin Rayuwa
Gwamnatin Legas Ta Kwace Baburan ‘Yan Arewa Masu Acaba 359
Gwamnatin Jihar Legas ta sake ?wace baburan ‘yan aca?a har 359, wa?anda ke kabu-kabu a bakin mayanka dabbobi da kuma gefen titin jirgin ?asa. Haka kuma an murtsike wuraren kwanan ‘yan share-wuri-zauna, domin a ?ara haskakawa da tsaftace wuraren. Hukumar Tsaftace Legas daTilasta da Tirsasa Bin Dokoki ta bayyana haka a ranar Laraba, ta ce wuraren da aka ruguje duk bukkoki ne da masu kwana waje suka kakkafa saboda kunnen ?ashin kangare wa dokar hukuma. Hukumar ta ce kuma an ?wace babura ne saboda ana zirga-zirgar ?aukar fasinja a daidai…
Read More‘Yan Najeriya Sun Yi Tir Da Karin Kudin Lantarki
Tun bayan da gwamnatin Najeriya ta sanar da ?arin ku?in wutar lantarki ga masu samun wutar lantarki ta tsawon sa’o’i 20 a kullum wa?anda suke ajin A kenan, ‘yan kasar na ci gaba da nuna damuwa da korafe-korafe da kuma tambayoyi kan lamari. Wannan matakin dai ya zo ne a daidai lokacin da ‘yan Najeriyar ke kokawa kan mawuyacin halin da tattalin arzikin kasar ke ciki da kuma tsadar rayuwa. A ranar Laraban da ta gabata ne hukumar da ke kula da wutar lantarkin a Najeriyar ta sanar da sabon…
Read MoreGwamnatin Tarayya Ta Bada Gagarumin Tallafi A Aikin Hajjin Bana
Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa a yayin da wa’adin da Hukumar Aikin Hajji ta sanya na biyan cikon kudin aikin hajjin bana yake cika zuwa karfe 12 na dare, sauki ya zo ma wasu maniyyata sakamakon Gwamnatin Tarayya da jihohin Kebbi, Kano, Kogi da Ogun suka ba da tallafi ga maniyyatan su don cika kudin aikin hajjin bana. Duk da haka dai, wasu maniyyatan sun ci gaba da neman Hukumar Walwala Da Jin Dadin Mahajjata na Jihohinsu da su mayar musu da kudin da…
Read MoreHoloko: Kwalejin Koyon Tukin Jiragen Sama Ba Ta Da Jirgi Ko Guda – Shugaban Kwaleji
Majalisar Tarayya ta sha alwashin cewa sai ta ?wato jiragen sama biyu ?irar Bell 206L4 BZB da kuma Bell M2062-L4, wa?anda mallakar Kwalejin Koyon Tu?in Jirage ne (NCAT) da ke Zariya, amma aka sayar da su ga wasu shafaffu da mai. Shugaban Kwamitin Bin Diddigin Kadarorin Gwamnati, Ademoyin Kuye ne ya bayyana haka, a lokacin zaman binciken da kwamitin ya yi, inda ya saurari bayanin yadda aka sayar da jiragen biyu. An yi zaman kwamitin sauraren sabar?alar a Majalisar Tarayya, ranar Alhamis, a Abuja. Kuye ya bayyana cewa abin damuwa…
Read MoreNajeriya Na Bisa Tsinin Mashi – Mataimakin Shugaban Kasa
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce abubuwa biyu ?an Najeriya ke bu?ata domin su fita daga kalubalen da ?asar ke fuskanta Ya ce har sai mutane sun ba gwamnati goyon baya tare da saka ya?inin cewa komai zai gyaru ne Najeriya za ta shawo kan matsalolinta. Shettima ya yi wannan jawabi ne a Abuja, a wajen bikin kaddamar da cibiyar nazarin harkokin kasa da kasa ta Najeriya a ranar Litinin. Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, a ranar Litinin, ya bukaci goyon bayan daukacin ‘yan Najeriya a kokarin da ake…
Read MoreKarin Kudin Aikin Hajji: Dubban Maniyyata Za Su Hakura Da Sauke Farali A Bana
Yayin da Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ?ara ku?in kujerar aikin Hajjin bana da miliyan ?aya da dubu ?ari tara, ana fargabar cewa da wuya maniyyatan bana su iya cikawa. A ranar Lahadi ne hukumar alhazan ta sanar da ?arin tana cewa hakan ya faru ne sakamakon tashin farashin dala, wadda da ita ce ake yin ?iyasin dukkanin abubuwan da maniyyata ke bu?ata a Saudiyya. Wannan ne karo na biyu da hukumar alhazan ke ?ara ku?in kujera a bana, abin da ya sa ake ganin da wuya a gudanar da…
Read MoreHajjin Bana: Kudin Kujera Ya Haura Naira Miliyan Takwas – Hukumar Alhazzai
Rahoton dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewa hukumar shirya aikin Hajji ta ?asa ta fitar da sabon farashin ku?in Hajjin Bana kamar haka: Daga yau 24 ga watan Maris Maniyyata daga shiyyar Adamawa/Borno za su biya Naira milyan N8,225, 464.74 Maniyyata daga shiyyar Arewa za su biya Naira milyan N8, 254, 464.74 Sai maniyyata daga jihohin shiyyar Kudu za su biya Naira milyan N8, 454, 464.74. Karamar kujera kuma ta tafi Naira miliyan 6.6. Tuni dai majalisar koli ta harkokin addinin Musulunci ta nuna damuwa gami…
Read MoreGobara Ta Hallaka Wata Daliba A Jami’ar Jihar Yobe
Allah ya yiwa wata dalibar jami’ar tarayya da ke Gashua (FUGA) mai suna Shamsiyya Murtala rasuwa bayan tashin gobara a dakin kwanan dalibai a jami’ar. Wannan mummunan lamarin ya auku ne a ranar Asabar 23 ga watan Maris na wannan shekarar, kamar yadda rahoto ya bayyana.Wutar ta kama ne a dakin kwanan dalibai a lokacin da dalibar ke barci mai nauyi. An ruwaito cewa, sauran dalibai sun yi kokarin ceto ta daga wutar, amma suka gaza fasa kofar dakin don samun damar shiga. Asibitin kwararru na Gashua ne ya tabbatar…
Read MoreNa Tayar Da Matattu Sama Da 50 Bayan Sun Mutu Murus A Coci Na – Fasto Chris
Babban malamin Cocin Christ Embassy, Chris Oyakhilome, ya tada kura bayan kalaman da ya yi a baya-bayan nan, lamarin da ya janyo cece-kuce a shafukan sada zumunta. A yayin wata addu’ar waraka da ya yi na kwanaki uku a kafar LoveWorld USA, faston mai shekaru 60 ya tabbatar da cewa cocinsa dawo da matattu sama da 50. Wannan lamari mai ban mamaki dai ya faru ne daga ranar 15 zuwa 17 ga Maris, 2024, inda ya ja hankali da muhawara a duniya. Mun tada matattu sama da 50, inji fasto…
Read MoreSaudiyya Ta Hana ‘Yan Najeriya Bizar Umrah
Dubban ‘yan Najeriya da ke da niyyar tafiya Umrah a wannan wata na Ramadana babu lallai burinsu ya cika saboda rashin biza daga kasar Saudiyya. Wannan ya biyo bayan wani sabon tsarin bayarda biza da ?asar ta Saudiyya ta fito da shi. Kawo yanzu cikin wa?anda suka biya ku?in tikiti da biza ya ?uri ruwa. Tuni ta bayyana ga masu jiragen sama cewa bana ba za su samu kasuwa kamar yadda suka saba yi ba. Kazalika, masu masaukin ba?i da ke da ?akunan haya na masu Umara da aikin Hajji…
Read MoreDa Dumi-Dumi: Abba Gida-Gida Ya Cigaba Da Rusau A Kano
Rahotannin dake shigo mana daga Jihar Kano na bayyana cewa wasu mazauna garin Gurin Gawa da ke karamar hukumar Kumbotso sun rasa matsuguni yayin da motar rusau ta gwamnatin Kano ta dira kan gidajensu. A ranar Lahadi ne hukumar tsare-tsare da raya birane ta jihar Kano (KNUPDA) ta rusa gidaje da dama a garin, kamar yadda Leadership ta ruwaito. Wannan rusau dai na zuwa ne duk da umarnin babbar kotun jihar Kano, wadda ta dakatar KNUPDA daga rusa gine-ginen al’umma a yankin. Da yake zantawa da manema labarai a ranar…
Read MoreKano: Ana Cigaba Da Yaba Mai Sana’ar POS Da Ya Mayar Da Miliyan 10 Da Aka Tura Mishi Bisa Kuskure
Wani mai sana’ar POS a Unguwar Kurnar Asabe da ke Jihar Kano ya mayar da kusan naira miliyan 10 da wani kwastomansa ya yi kuskuren tura masa a maimakon dubu 10. Lamarin dai ya faru ne yayin da abokin kasuwancinsa ya yi yunkurin tura wa mai POS din naira dubu 10, kamar yadda rundanar ’yan sanda Kanon ta bayyana a wata sanarwa da ta fitar ranar Alhamis. Rundunar ta ce lamarin ya faru ne tun a watan Disamba na shekarar 2023, lokacin da mai sana’ar POS mai suna Mohammed Sani…
Read MoreRamadan: Gwamnatin Katsina Ta Karya Farashin Hatsi
Labarin dake shigo mana daga Jihar Katsina na bayyana cewa a yayin da ake tsadar kayan abinci a Najeriya, gwamnatin Katsina tare da ha?in gwiwar ?ananan hukumomin jihar 34 sun ware sama da Naira biliyan 10 domin saye da bada tallafin hatsi domin rabawa ga marasa galihu a cikin watan Ramadan. Gwamna Dikko Radda na jihar Katsina ne ya tabbatar da hakan a yayin ?addamar da kwamitocin a matakin jiha da na ?ananan hukumomi da aka ?orawa alhakin sa ido kan yadda za a raba kayan a ranar Asabar.A cewar…
Read MoreKano: Hukumar Tace Fina-Finai Ta Bada Umarnin Rufe Gidajen Gala
Hukumar tace Fina-finai da ?ab’i ta Jihar Kano ta umarci rufe dukkan gidajen gala a fadin jihar. Shugaban hukumar a jihar, Abba El-Mustapha shi ya bayyana haka a ranar Lahadi 10 ga watan Maris a shafinsa na Facebook. Abba ya ce an dauki wannan matakin ne saboda shirye-shiryen da ake yi na tukarar watan azumin Ramadan. Daukar matakin ya biyo bayan wata ganawa da shugaban hukumar ya yi da jagororin kungiyar masu gidajen gala da ke jihar. El-Mustapha ya ce dokar za ta fara aiki ne daga ranar Lahadi 10…
Read MoreBabu Wata Karuwa Ko Dan Daudu Da Za Su Sarara A Kano – Daurawa
Rahoton dake shigo mana daga Jihar Kano na bayyana cewa Shugaban Hukumar Hisbah Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya lissafa abubuwa 3 da za su yi a inganta aikinsu a Kano Bayan ban hakuri da zaman sulhu, Daurawa ya ba ‘yan daudu da karuwai wa’adin barin Kano Sai dai kuma, yayin da wasu ke ganin abubuwan da suka faru a baya za su kawo cikas ga ayyukan Hisbah, Shehin malamin ya ce hakan karfafa masu gwiwar kara kaimi kan ayyukansu ya yi. Daurawa ya kuma ce sun ba duk wasu masu…
Read MoreKano: Sheikh Daurawa Ya Koma Shugabancin Hisbah
Rahotannin dake shigo mana daga Jihar Kano na bayyana cewa Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya amince ya koma kan mu?aminsa a matsayin Kwamandan Hukumar Hisbah domin ci gaba daga inda ya tsaya. Daurawa ya amince da hakan ne bayan da malamai suka shiga suka suhulta tsakaninsu da Gwamnan Kano, Abba Kabir. Tun farko, Malam Daura ya sanar da ajiye mu?amin nasa cikin wani faifain bidiyo da aka ya?a inda aka ji shi yana bai wa Gwamna Kabir ha?uri kana daga bisani ya ce ya ajiye shugabancin Hisbah. Gwamna Kabir ya…
Read MoreKaduna: Kungiyar NURTW Ta Tallafawa Direbobi 360
Daga Ibrahim Ammani Kungiyar direbobin sufuri ta kasa NURTW reshen jihar Kaduna ta tallafawa direbobi 360 da kudi naira miliyan 3 da dubu 600 da kuma atamfofi da shaddoji domin rage musu radadin rayuwa. Kungiyar tace daga ciki akwai mata guda 21 da suka amfana da tallafin wanda hakan Yana daga cikin matakan da kungiyar take dauka na tallafawa rayuwar direbobi. A jawabin da ya gabatar shugaban kungiyar na jihar Kaduna Alhaji Aliyu Tanimu Zaria, (Magajin Makaman Gusau) yace sun bayar da tallafin ne ga direbobi wadanda suka sadaukar da…
Read MoreKano: Akwai Kurakurai A Ayyukan Hukumar Hisbah – Gwamna
Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, ya gargadi Hukumar Hisbah ta jihar da ta rika taka-tsan-tsan wajen kiyaye hakkin dan Adam a yayin aiwatar da ayyukanta. Gwamnan ya yi wannan kiran ne a wani ?angare na jawaban da ya gabatar yayin ganawa da malamai a Fadar Gwamnatin Kano. Gwamnan wanda ake yi wa lakabi da Abba Gida-Gida, ya bayyana damuwarsa kan wani bidiyo da ya ce ya yi arba da shi kan yadda Hukumar Hisbah ta jihar ke gudanar da ayyukanta wajen kama wadanda ake zargi da aikata laifuka masu nasaba…
Read MoreMinistar Mata Ta Shawarci Mata Su Guji Sa In Sa Da Maza A Wannan Lokaci
Ministar harkokin mata, Uju Kennedy-Ohaneye, ta shawarci mata a kasar da su daina yin sa’insa ko fada da mazansu yayin da sabani ya gibta tsakaninsu a gida. Ministar ta bayar da shawarar ne a yayin wani taron kwamishinonin ma’aikatun mata na jihohi a Najeriya, wanda aka yi a ranar Laraba a Abuja. Kennedy-Ohaneye ta ce guje wa cacar baki zai hana cin zarafi da ka iya kai ga jin rauni ko mutuwa. “Ina kuma rokon mata akan kada su tsokano rigima, koda kuwa a gida ne. Ku zauna lafiya a…
Read More