Zan Iya Kawar Da ‘Yan Boko Haram Ni Ka?ai – Igboho

Shahararren mai rajin kare hakkin Yarbawa Sunday Adeyemo wanda aka fi sani da Sunday Igboho ya bayyana cewa yana da cikakken shiri da mai ?arfi domin yaki da Boko Haram ba tare da goyon bayan gwamnati ba. Igboho ya yi wannan bayanin ne a wata hira ta bidiyo da aka fitar a shekarar 2020. Ya ce: “Abin da zan yi amfani da shi wajen yaki da Boko Haram, ina da shi tuni.” Bidiyon ya sake bayyana bayan da tsohon Sanata mai wakiltar Kaduna ta Tsakiya, Shehu Sani, ya yi kira…

Read More

Kisa Ne Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sulhu Ba – El Rufa’i

A daidai lokacin da ‘yan bindiga ke ci gaba da kai hare-hare babu kakkautawa a jihohin Arewa, Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya ce rashin hadin kai tsakanin gwamnonin yankin na da daga cikin abin da ya sa aka kasa shawo kan matsalar. A hirarsa da BBC gwamnan ya ce shi yana da ra’ayin a bude ma ‘yan bindigar wuta kuma babu batun sulhu tsakanin gwamnatinsa da masu garkuwa da mutane. Kalaman El Rufa’i na zuwa ne bayan jawabin da sanannen malamin addinin Musulunci Dr. Ahmad Gumi ya yi, inda…

Read More

Taraba: An Sace Shugaban ?ungiyar Kwadago

Wasu da ba a san ko su waye ba, sun sace shugaban kungiyar kwadago reshen jihar Taraba mai suna kwamred Peter Jediel. An sace shugaban kungiyar ne da sanyin safiyar lahadin a gidansa da ke yankin Sunkani karamar hukumar Ardo-Kola. Kanin shugaban kungiyar Mr Fidelis Jediel ya shaida wa ‘yanjarida cewa ‘yan bindigar sun mamaye hanyar zuwa gidan, suka yi awon-gaba da shi. Har ya zuwa lokacin hada labarin, babu wata tartibiyar magana daga hukumar ‘yansandan jihar. Harkar satar mutane tare da yin garkuwa da su na nema zama ruwan…

Read More

Masu Tallar Nono Na Safarar Muggan Kwayoyi Ga ‘Yan Bindiga – Tambuwal

Gwamnan jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal ya yi zargin cewa matan da ke tallar fura da nono na safarar mugga kwayoyi da sauran kayan bukatun yau da kullum ga ‘yan ta’addan dake cikin daji, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito. Gwamna Tambuwal ya yi wannan zargin ne a lokacin da ya karbi tawagar shehin malami Dr Ahmad Gummi a Sokoto. Gwamna Aminu Waziri Tambuwal yace ya kamata mutane su saka lura ga wadanda ke kai kawo cikin gari zuwa daji domin a hana bazuwar makamai da ke tunzura ayyukan…

Read More

Da ?umi-?umi: ‘Yan Bindiga Sun Bindige Mutum 18 A Kaduna

Wasu ?an bindiga sun kai hari Tashar Ka?anta a yankin Kutemeshi na ?aramar hukumar Birnin Gwari da ke jihar Kaduna inda suka kashe mutum 19 a ranar Asabar. Mazauna yankin sun ce ?an bindigar sun shigo ne misalin ?arfe 5 na yamma inda suka bu?e wuta suka abka shagunan mutane suka kwashi kayayyaki da suka ha?a da wayoyin salula. Bayan kashe mutum 19, sun kuma raunata mutum 10, kamar yadda wani mazauni yankin ya shaida wa BBC. Ya ce kuma yanzu da safiyar Lahadi ake shirin yi wa mamatan jana’iza.…

Read More

Zamfara: ‘Yan Bindiga Za Su Mi?a Wuya Kwanan Nan – Matawalle

Gwamna Bello Mohammed Matawalle na jihar Zamfara, ya ce an kammala tattauna wa da babban ?an shugaban ‘yan bindigan da aka kashe, Buharin Daji, wanda ya cigaba da jagorar ‘yan Bindiga tun bayan kisan da aka yi wa mahaifinsa. Gwamnan ya kara da cewa ?an Buharin Daji, mahaifiyarsa da wani babban jagoran ‘yan bindiga a Zamfara za su ajiye makamai, su rungumi sulhu da zaman lafiya da sauran jama’ar Jihar. Gwamnan na Zamfara ya yi wannan jawabi ne a lokacin da ya zauna da tawagar shehin malamin nan na Kaduna,…

Read More

Zamfara: ‘Yan Bindiga Za Su Mi?a Wuya Kwanan Nan – Matawalle

Gwamna Bello Mohammed Matawalle na jihar Zamfara, ya ce an kammala tattauna wa da babban ?an shugaban ‘yan bindigan da aka kashe, Buharin Daji, wanda ya cigaba da jagorar ‘yan Bindiga tun bayan kisan da aka yi wa mahaifinsa. Gwamnan ya kara da cewa ?an Buharin Daji, mahaifiyarsa da wani babban jagoran ‘yan bindiga a Zamfara za su ajiye makamai, su rungumi sulhu da zaman lafiya da sauran jama’ar Jihar. Gwamnan na Zamfara ya yi wannan jawabi ne a lokacin da ya zauna da tawagar shehin malamin nan na Kaduna,…

Read More

Ba Fulani Suka Kai Hari Sakandaren Jihar Kogi Ba – Gwamnati

Gwamnatin jihar Kogi ta karyata rahotannin da ke cewa makiyaya Fulani ne suka kona makarantar sakandare ta Illuke Bunu inda ta ce kona daji ba bisa ka’ida bane ya janyo gobarar, sa?anin labaran da wasu ke ya?awa na cewar harin Fulani ne. Hakan ne kunshe ne cikin sanarwar da kwamishinan watsa labarai na jihar, Mista Kingsley Fanwo ya fitar mai taken, ‘Rahoton farko game da kona makarantar sakandare ta Iluke Bunu.’ Ba makiyaya bane suka bankawa makarantar sakandare wuta. Sanarwar ta kuma ce gwamnatin za ta cigaba da zurfafa bincike…

Read More

Abinda Na Gani A Dajin Zamfara Ya Hanani Runtsawa – Dr. Gumi

Fitaccen malamin addinin musulunci, Sheikh Dr. Ahmad Abubakar Mahmoud Gumi ya bada labarin tafiyar da ya yi zuwa sansanin wasu ‘yan bindiga a dajin jihar Zamfara. Ganin yadda ake fama da matsalar rashin tsaro a Arewa maso yammacin Najeriya, babban malamin ya shiga inda ‘yan bindiga su ke, ya na lallabarsu, akan su rungumi matakin zaman sulhu ba ?aukar bindiga ba. Da yake yi wa gwamnan Zamfara, Alhaji Bello Matawalle, bayanin abin da ya gani, Malamin ya bayyana cewa tsagerun ‘yan bindigan sun zama ‘yan ta’adda ri?a?ku fiye da yadda…

Read More

An Kara Wa Shugaban ‘Yan Sanda Wa’adi

Babban Shugaban rundunar ‘Yan Sanda ta kasa Mohammed Adamu, a ranar Alhamis, ya nada babban jami’in sa (PSO), Idowu Owohunwa, da jami’in Ilimi na rundunar, Rabi Umar ado, matsayin kwamishinan ‘yan sanda a hedikwatar rundunar da ke Abuja. Hakanan an nada ACP (Dr.) Adegbite Tunde Titus; ACP (Dakta) Chinonyerem Lawrence Welle da kuma Mataimaki na Musamman ga Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar, DSP Aderoju Olagunju, da sauransu. Jami’an ‘yan sandan da aka yiwa nadin suna daga cikin sabbin ayyukan hukumar ‘yan sanda da aka daga darajar su, kamar yadda…

Read More

An ?ara Wa Shugaban ‘Yan Sanda Wa’adin Watanni Uku

Babban Shugaban rundunar ‘Yan Sanda ta kasa Mohammed Adamu, a ranar Alhamis, ya nada babban jami’in sa (PSO), Idowu Owohunwa, da jami’in Ilimi na rundunar, Rabi Umar ado, matsayin kwamishinan ‘yan sanda a hedikwatar rundunar da ke Abuja. Hakanan an nada ACP (Dr.) Adegbite Tunde Titus; ACP (Dakta) Chinonyerem Lawrence Welle da kuma Mataimaki na Musamman ga Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar, DSP Aderoju Olagunju, da sauransu. Jami’an ‘yan sandan da aka yiwa nadin suna daga cikin sabbin ayyukan hukumar ‘yan sanda da aka daga darajar su, kamar yadda…

Read More

Kiran Fulani Da Sunan ‘Yan Ta’adda Na Iya Haifar Da Ya?i – El Rufa’i

Gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya yi gargadi game da yiwa dukkan Fulani makiyaya kudin goro a matsayin masu laifi kuma masu kisan kai, ko kiran su ‘yan ta’adda kai tsaye, inda yace hakan ba ?aramin kuskure ba ne da zai iya haifar da gagarumar matsala a Najeriya. El-Rufai ya ayyana cewa aikata fashi da makami da sauran miyagun ayyukan na ta’addanci sun zama wata masana’anta kuma dole ne ‘yan Najeriya su hada kai don kawo karshen sa gaba ?aya a ?asar. Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin karbar bakuncin…

Read More

A Shirye Muke Mu Gayyaci Sojin Ketare A Gama Da Najeriya – Shugaban ‘Yan Bindiga

Shugaban ‘yan ta’addan Jihar Zamfara dake yankin Arewa maso Yammacin Najeriya, Kachalla Turji, ya ce a shirye kungiyarsa take tayi kira da neman goyon bayan kasashen waje don yaki da dagula Najeriya. An ji yi muryar Shugaban ‘yan ta’adda Turji a cikin wani faifan bidiyo da aka yada a kafar Facebook suna tattauna akan korafe-korafen da suke ci gaba na kashe-kashe, da satar mutane da kungiyoyin masu satar shanu a yankin. Shugaban ‘yan Bindigar ya yi magana ne akan ?arfin da kungiyar tasa ke dashi da buwayarta, da kuma kokarin…

Read More

Matsalar Tsaro: A Bari ‘Yan Najeriya Su Mallaki Bindigogi – Gwamnan Taraba

Gwamnan jihar Taraba, Darius Ishaku, ya bukaci gwamnatin tarayya ta bari mutane su mallaki bindigogin kansu domin kare kansu da iyalansu saboda yadda matsalar tsaron da kasar ke fuskanta. Gwamna Ishaku ya bayyana haka ne ranar Talata yayinda shugabannin kananan hukumomin jihar suka ziyarceshi bayan jana’izar daya daga cikinsu da ‘yan bindiga suka kashe. Gwamnan ya yi alhinin tsanantan rashin tsaro, inda Najeriya bata taba shiga irin wannan halin ba. “Matsalar tsaro a kasar nan tayi munin da bata taba yi ba kuma ya zama wajibi mu tashi tsaye. Mu…

Read More

Babu Dalilin Bincikar Tsoffin Shugabannin Tsaro – Fadar Shugaban ?asa

Ministan yada labarai da Al’adu na kasa, Lai Muhammad, ya ce babu bukatar gudanar da bincike ga tsaffin hafsoshin tsaro da aka sauke saboda a cewarsa ko wace ma’aikata tana da dokokin hukunta laifuka. Ministan wanda ya bayyana haka lokacin da yake Magana a wani shirin talabijin ranar Talata, ya kuma caccaki masu kiran kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC ta bincike tsaffin hafsoshin, yana mai bayyana su a matsayin marasa kishin kasa. A makon jiya ne dai shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada sabbin hafsoshin tsaron da suka…

Read More

Katsina: ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane 14

A ranar Talata ‘yan bindiga suka kashe mutum 14 a karamar hukumar Sabuwa dake jihar Katsina. Lamarin ya afku ne sakamakon wani direban amalenke ya je debo yashi da keken shanunsa, inda ya yi karo da yan ta’adan suka kwance masa shanun da tsiya suka yi gaba da su Hakan ne ya sa ‘yan gari suka bazama cikin dajin domin ganin barayin sun dawo da shanun amma abin ya gagara, wanda ya ja kashe mutum 14 ‘yan cikin gari da suka je kwato shanun. Har aka gama gwagwarmayar, ba a…

Read More

Zanga-Zangar A Kori Fulani Ta ?arke A Edo

Bayan guguwar fitina ta kyamatar Fulani da ta ?arke a yankunan Jihohin Yarbawa dake Kudu maso yammacin ?asar nan, dubban Mata ne suka fito suka cika manyan titunan dake Benin City babban birnin Jihar Edo suna kiran a gaggauta korar Fulani daga jihar. Matan sun bayyana cewa yanzu basu iya zuwa gonakinsu domin noma, basa iya fita kasuwanci sannan ‘ya’yan su ba sa samun zuwa Makarantu sakamakon ayyukan ta’addanci da Fulani ke aikatawa a yankin na kisa da garkuwa da Mutane a kusan kullum suna kar?ar kudin fansa. Masu Zanga-Zangar…

Read More

Korar Fulani: Martanin Arewa Ba Zai Yi Kyau Ba – Tofa

Sanannen Dattijo a yankin Arewa Alhaji Bashir Usman Tofa, ya yi gargadin cewa wadanda ke neman tada rikicin kabilanci a kasar su daina domin kare afkuwar babban tashin hankali da zai haifar da wargajewar Najeriya gaba ?aya. Ana zaman dar dar ne a kasar tun bayan da aka ba makiyaya wa’adin kwanaki su fice daga yankin kudu maso yamma kan karuwar hare hare da rashin tsaro. Sunday Igboho, wani mai kare hakkin Yarbawa ya fara tada rikicin a watan Janairu a jihar Oyo wadda ya janyo rasa rayyuka da dukiyoyi.…

Read More

Korar Fulani: Martanin Arewa Ba Zai Yi Kyau Ba – Tofa

Sanannen Dattijo a yankin Arewa Alhaji Bashir Usman Tofa, ya yi gargadin cewa wadanda ke neman tada rikicin kabilanci a kasar su daina domin kare afkuwar babban tashin hankali da zai haifar da wargajewar Najeriya gaba ?aya. Ana zaman dar dar ne a kasar tun bayan da aka ba makiyaya wa’adin kwanaki su fice daga yankin kudu maso yamma kan karuwar hare hare da rashin tsaro. Sunday Igboho, wani mai kare hakkin Yarbawa ya fara tada rikicin a watan Janairu a jihar Oyo wadda ya janyo rasa rayyuka da dukiyoyi.…

Read More

Turnu?u: An Raba Rana Tsakanin Aisha Da Kanu

An raba rana a tsakanin fitacciyar ‘yar gwagwarmayar nan, Aisha Yesufu da jagoran matasan Inyamurai Nnamdi Kanu, inda suka bu?e wa juna wuta a kafar sada zumuntar zamani ta Twitter. A ranar Lahadi, 31 ga watan Janairu Nnamdi Kanu ya wallafa wani bidiyo a shafinsa na Facebook inda yake nuna jami’an tsaron kudu, ESN, suna hantarar Fulani a sansaninsu dake Isuikwuato, jihar Abia, inda suka yi ta fatattakarsu suna kashe musu shanu. Wannan bidiyon ya fusata Yesufu, inda ta caccaki lamarin har take cewa hakan bai dace ba. Kamar yadda…

Read More