Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Lalacewar da tsarin samar da hasken lantarki ke yi ya ci gaba da saka ‘yan Najeriya cikin duhu.
Masu amfani da lantarki a gidajensu ko a wuraren aiki a biranen Legas da Enugu da Ibadan da Anambra da Abuja na rayuwa cikin wannan duhun saboda na’urorin samar da hasken lantarki sun sake gazawa.
Wannan lamarin da ke faruwa ya zama ruwan dare gama duniya, kuma kamfanonin da ke samarda lantarki sun tabbatar da haka.
Yini na biyu ke nan a jere da ake samun wannan matsalar ta lalacewar na’urorin samar da lantarki a fadin Najeriya.
Matsalar na faruwa ne dadai lokacin da Najeriya ke fuskantar matsalar man fetur da wanda jirgin sama ke amfani da shi.
