Da Dumi-Dumi: An Sanar Da Sake Bude Makarantu A Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanar da sake bude makarantu a jihar daga ranar Laraba 18 ga watan Agusta 2021.

Ko da yake tace komawar za ta shafi yan aji uku na sakandare ne kadai.

Kwamishinan ilimi na jihar ne ya bayyana hakan a wata sanarwa ranar Laraba.

Yace daliban za su rika zuwa makarantar ne da da kayan gida.

A satin da ya gabata gwamnatin jihar ta rufe makarantu sakamakon ayyukan soja da suke ta gudana akan yan fashi a arewacin Najeriya.

Gwamnati ta amine komawar yan aji uku na sakandare wanda za su rubuta jarabawar NECO BECE daga 23 ga Agusta zuwa 6 ga watan Satumba 2021.

Don haka makarantun sakandare za su koma aiki saboda yan aji uku kadai daga 18 ga watan Agusta sannan kuma ba za su saka kayan makaranta ba a cewar kwamishinan.

Related posts

Leave a Comment