‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum 28 A Kudancin Kaduna

Mutum 28 sun mutu, an jikkata wasu da dama a harin ?an bindiga a kauyukan Malagum 1 da Sokwong na Karamar Hukumar Kaura ta Jihar Kaduna. Jaridar Aminiya ta rawaito cewa Sakataren Karamar Hukumar, Raymond Ibrahim, ya ce ?an bindiga sun far wa kauyen Sakwong ne da misalin karfe 12 na dare kafin wayewar garin Lahadi, su na harbi kan mai uwa da wabi tare da cinna wa gidade da dukiyoyi wuta. Ya ce, “Da safen yau muka dawo daga wurin muka ga gawarwaki tara, daga nan muka karasa zuwa…

Read More

Harin Sojin Sama Ya Hallaka Mutum 64 A Zamfara

Al’ummar garin Mutunji dake jihar Zamfara suna cikin halin zulumi da tashin hankali, bayan asarar rayuka mafi muni da garin bai ta?a ganin irin sa ba. Rahotanni daga garin sun ce a ?alla mutum 64 ?an garin ne suka rasa rayukansu bayan da wani jirgin soja ya jefa bam a wani waje da ?an bindiga suka yi mafaka. Wani mazaunin garin da ya nemi a sakaya sunansa ya tabbatar wa BBC cewa dukkan wa?anda suka mutun maza ne, mafi yawan su ?ananan yara, sai kuma matasa da tsofaffi. “An yi…

Read More

‘Yan Bindiga Sun Kaddamar Da Sabon Hari A Jihar Borno

Labarin dake shigo mana daga Maiduguri babban birnin Jihar Borno na bayyana cewar wata mata mai juna biyu, Mary Barka ta rasa ranta yayin da wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, dauke da bindigu kirar AK 47 suka yi dirar mikiya kauyen Pelachiroma na karamar hukumar Hawul dake jihar Borno. Ba tare da jinkiri ba shugaban mafarautan yankin Muhammad Shawulu Yohanna yayi nasarar cafkesu gami da mika su ga shugaban ‘yan sandan yankin Hawul, Habila Lemaka. Kamar yadda Yohanna, shugaban ‘yan sa kai da mafarauta ya bayyana…

Read More

Sai An Biya Miliyan 100 Kafin Mu Saki ‘Yan Matan Kwalejin Yawuri – ‘Yan Bindiga

Fitaccen ?an ta’addan jihar Zamfara Dogo Gide da yayi garkuwa da dalibai mata ‘yan kwalejin Yawuri dake jihar Kebbi ya rantse ba zai saki sauran wadanda suka rage a hannunsa tare da malaman su har sai an kai masa diyyar naira miliyan 100 da ya bukata. Wannan matsayi ya biyo bayan wani sautin hirar da aka nada tsakanin wani daga cikin mahaifin dalibar dake hannunsa da mahaifiyarsa wadda ta bukaci ya sake sauran wadanda yayi garkuwar da su. Gide wanda yayi kaurin suna wajen kai munanan hare hare yana hallaka…

Read More

Shekau Ya Mutu Ya Bar Mata 83 A Duniya – Kwamandojin Boko Haram

Rahotannin dake shigo mana daga Maiduguri babban birnin Jihar Borno na bayyana cewar wasu tsoffin Kwamandojin Boko Haram sun sanar da cewar shugabansu Abubakar Shekau ya mutu ya bar kwarkwara 83, lokacin da ya bar duniya. Mai ba Gwamnan Jihar Borno shawara a kan harkokin tsaro, Janar Abdullahi Ishaq ya sanar da wannan labari, yayin da ya bayyana cewar wasu tubabbun Kwamandojin Boko Haram da suka aje makamansu ne suka shaida masa. Janar Ishaq ya ce lokacin da suka karbi wasu daga cikin tubabbun a garin Bama ne daya daga…

Read More

Dalilina Na Yin Kisa Da Garkuwa Da Mutane – Turji

Rahotannin dake shigo mana daga Gusau fadar Gwamnatin Jíhar Zamfara na bayyana Tashar Trust TV ta zanta da kasurgumin jagoran ‘yan bindiga Bello Turji, inda ya bayyana dalilin da yasa ya dau bindiga ya fara ta’addanci. A cewarsa, rashin adalcin da akewa Fulani Makiyaya da wula?anta su tare da mayar dasu Saniyar ware cikin al’umma ya tilasta masa daukar bindiga domin ?aukar fansa. A hirar, ya bayyana cewa a kasuwar Shinkafi ya fara ganin yadda aka yiwa dan Adam yankan rago. Yace jami’an Yan Sa Kai suka kawo wani mutumi…

Read More

Za A Rufe Sansanonin ‘Yan Gudun Hijira – Gwamnatin Tarayya

Labarin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Gwamnatin tarayya ?ar?ashin jagorancin shugaban ?asa Muhammadu Buhari ta ce tana shirin rufe sansanonin ‘yan gudun hijira a fadin ?asar. Babbar kwamishiniya a ma’akatar kula da ‘yan gudun hijira da kuma ‘yan cirani, Imaan Sulaiman-Ibrahim ce ta bayyana hakan a ranar Juma’a yayin raba wa ‘yan gudun hijra guda 100 kayakin yin sana’o’i a wasu sansanoni da ke Abuja, babban birnin ?asar. Ta ce wadanda aka raba wa kayayyakin suna samun horo a fannin sana’o’i daban-daban domin samun kwarewa.…

Read More

Borno: Zulum Ne Ya Sa Na Mika Wuya – Kwamandan Boko Haram

Labarin dake shigo mana daga Maiduguri babban birnin jihar Borno na bayyana cewar wani kwamandan Boko Haram da ya mika wuya mai suna Mallam Adamu Rugurugu, ya bayyana dalilin da yasa ya ajiye makaman yakinsa. Rugurugu ya bayyana cewa ya yanke shawarar fitowa daga jeji tare da mayakansa da dama saboda roko da shiga lamarin da Gwamna Babagana Zulum na jihar Borno ya yi. Da yake magana a sansanin da aka ajiye fiye da yan ta’adda 14,000 da suka mika wuya tare da iyalinsu a Maiduguri, Rugurugu ya ce ya…

Read More

Katsina: ‘Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Mutane A Masallaci

Labarin dake shigo mana daga jihar Katsina na bayyana cewar ‘Yan bindiga sun kai hari tare da sace masallata kusan 20 a wani masallaci a ?auyen Maigamji da ke yankin ?aramar hukumar Funtua a jihar. R?ahotonnin sun ce maharan sun kai farmaki masallacin ne ranar Asabar da daddare lokacin da masallatan suka taru domin gudanar da sallar Isha’i. Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar katsina SP Gambo Isah ya shaida wa BBC cewa an raunata limamin masallacin tare da wani mutum guda, an kuma sallamo su daga asibiti…

Read More

Zamfara: Bello Turji Ya Kalubalanci Soji Kan Gaza Kashe Shi

Labarin dake shigo mana daga jihar Zamfara na bayyana cewar Bello Turji Kachalla, wanda aka fi sani da Turji, shahararren ‘dan ta’adda ne kuma shugaban ‘yan bindiga dake addabar jihohin Zamfara, Sokoto da Niger yace gwamnatin Najeriya bata da ra’ayin kawo karshen ta’addanci saboda wasu jami’an suna amfana daga shi. Turji ya sanar da hakan matsayin martani ga luguden wutan da sojoji suke yi a gidansa kuma ya zargi gwamnatin da tunzurasu ta yadda har zasu karya yarjejeniyar zaman lafiya da suka yi da mazauna yankin. Bello Turji a farkon…

Read More

Zamfara: Bello Turji Ya Kalubalanci Soji Kan Gaza Kashe Shi

Labarin dake shigo mana daga jihar Zamfara na bayyana cewar Bello Turji Kachalla, wanda aka fi sani da Turji, shahararren ‘dan ta’adda ne kuma shugaban ‘yan bindiga dake addabar jihohin Zamfara, Sokoto da Niger yace gwamnatin Najeriya bata da ra’ayin kawo karshen ta’addanci saboda wasu jami’an suna amfana daga shi. Turji ya sanar da hakan matsayin martani ga luguden wutan da sojoji suke yi a gidansa kuma ya zargi gwamnatin da tunzurasu ta yadda har zasu karya yarjejeniyar zaman lafiya da suka yi da mazauna yankin. Bello Turji a farkon…

Read More

Shugaban ‘Yan Sanda Ya Nemi Kotu Ta Janye Hukuncin Daurin Da Ta Yi Mishi

Sufeto Janar na ‘Yan Sandan Najeriya IGP Usman Alkali Baba ya shigar da ?udirin neman jingine umarnin kotu da ya ?aure shi wata uku a gidan yari, yana mai cewa bai raina umarnin kotun ba. Cikin ?orafin da ya gabatar a gaban Babbar Kotun Tarayya a Abuja ranar Alhamis, shugaban ‘yan sandan ya ce ba a ?ar?ashin shugabancinsa aka aikata laifin da kotun ta yi hukunci a kansa ba kuma “ba a sa?a wa umarnin kotu ba”. A makon nan ne Babbar Kotun Tarayya ta ba da umarnin kama babban…

Read More

Kotu Ta Bada Umarnin Kama Shugaban Dakarun Soji

Rahotannin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar wata babbar kotun tarayya da ke zama a Minna, jihar Neja, ta bayar da umurnin kama babban hafsan sojin kasa Janar Faruk Yahaya bisa laifin rashin grimama kotu. Mai shari’a Halima Abdulmalik, wadda ta yanke hukuncin ta kuma bukaci da a kulle Janar Yahaya a gidan gyara hali na Minna saboda saba ma wani umurnin kotu na ranar 12 ga watan Oktoba, 2022. Wannan na zuwa ne kwanaki kadan bayan da wata babbar kotun da ke zamn ta a…

Read More

Kotu Ta Daure Dalibin Da Ya Ci Zarafin Aisha Buhari

Rahoton dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar an gabatar da Aminu Muhammad da ake zargi da cin mutuncin Uwargidan Shugaban ?asa Aisha Buhari gaban kotu jiya Talata, kuma tuni ma an garzaya da shi gidan yari. Lauyan dalibin CK Agu ya tabbatar wa da BBC cewa an gurfanar da wanda yake karewar a gaban wata kotu da ke Abuja kuma bai amsa laifin da ake zargin shi da aikatawa ba. Mr Agu ya ce tun ranar 25 ga watan Nuwamba suka nemi a bada Aminu beli…

Read More

Kotu Ta Yanke Wa Sifeto Janar Na ‘Yan Sanda Daurin Watanni Uku A Kurkuku

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, a yau Talata ta yanke wa Sufeto-Janar, IGP, na ?an sanda, Usman Baba, zaman gidan yari na tsawon watanni uku, bisa zargin kin bin umarnin hukuncin da wata kotu ta yanke na kin mayar da wani jami’in dan sanda, Patrick Okoli, wanda aka yi wa ritaya ta ?arfi da yaji bakin aiki. Mai shari’a Bolaji Olajuwon, a hukuncin da ya yanke kan karar da lauyan Okoli, Arinze Egbo, ya shigar, ya kuma gargadi Baba kan rashin bin hukuncin da kotun farko ta yanke…

Read More

‘Yan Sanda Sun Nesanta Kansu Da Kama Matashin Da Ya Soki Aisha Buhari

Rundunar ‘yan sanda reshen jihar Jigawa, tace ba ta da hannu wajen cafke wani dalibi mai suna Aminu Muhammad da ake zargin tayi. Ana zargin Aminu Muhammad yana hannun dakarun ‘yan sanda bisa zargin da ake yi masa na cin mutuncin uwargidar shugaban kasa, Aisha Buhari. Da aka tuntubi ‘yan sandan jihar Jigawa, sun tabbatar da cewa Aminu Muhammad bai hannunsu, kuma ba su iya yin wani bayanin inda ya shiga ba. Kakakin rundunar jihar, DSP Lawan Shiisu ya shaidawa manema labarai cewa bai da labarin jami’an sanda sun dauke…

Read More

Ba Mu Janye Tuhumar Da Muke Yi Wa Tukur Mamu Ba – DSS

Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta musanta rahoton da ke yawo cewa ta janye ?arar data shigar kan Tukur Mamu, tsohon mai shiga tsakani da ‘yan ta’adda. Wani rahoton da ake ya?awa ya yi ikirarin cewa hukumar ta janye ?arar da ta shigar a babbar Kotun tarayya mai zama a Abuja, inda ta samu sahalewar tsare shi na kwana 60. Rahoton ya nuna Lauyan DSS, A. M Danlami ya shaida wa Mai shari’a Nkeonye Maha, jim ka?an bayan kiran ?arar, cewa hukumar ta jingine shari’ar. Amma a wata hira…

Read More

Borno: ISWAP Sun Karkashe Sojoji Da Fararen Hula

Labarin dake shigo mana daga Maiduguri babban birnin Jihar Borno na bayyana cewar ana fargabar wasu ‘yan ta’addan ISWAP sun kai farmaki sansanonin soji guda biyu a jihar sun tafka mummunar barna. A ecwar wani rahoton da AFP ta fitar jaridar Leadership kuwa ta tattaro, ‘yan ta’addan sun kai hare-haren ne a ranakun Juma’a da Asabar a wani sansanin soji da kuma gari, inda suka kashe sojoji tara. Hakazalika, an ce sun hallaka wasu ‘yan sanda biyu da kuma wani adadi na mutanen gari, kamar yadda wata majiya ta shaida.…

Read More

‘Yan Bindiga Sun Kaddamar Da Kazamin Hari A Jihar Kaduna

Labarin dake shigo mana daga jihar Kaduna na bayyana cewar wasu da ake zargi ‘yan bindiga ne ?auke da muggan makamai sun kashe mutum hudu a wani kauye ciki har da wani sabon malami a karamar hukumar Kajuru dake jihar ta Kaduna. Harin ya yi sanadin rayuka uku ciki har da wani shugaban matasa a daren ranar Lahadi. Mazaunin garin ya yi ?arin haske kan harin Within Nigeria ta tattaro cewa a harin na biyu a Tudun Mare ne aka kashe wani malami mai suna Elisha Arziki. Wani mazaunin garin…

Read More

Sojoji Sun Fitar Da Hotunan ‘Yan Ta’adda Da Ake Nema Ruwa A Jallo

Hedkwatar tsaro ta Najeriya, a ranar Litinin ta fitar da sunayen kwamandojin yan ta’adda 19 da ke adabar yankunan Arewa maso Gabas, Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya a kasar, inda ta ayyana nemansu ruwa a Jallo. Hedkwatar tsaron ta ce za ta ba da tukwicin Naira miliyan 5 ga duk wani dan Najeriya da ya bada bayanan yadda za a kama yan ta’addan, ta bukaci al’umma su tuntube ta a wannan lambar 09135904467. Ta ce hakan ya zama wajibi ne domin cigaba da kawar da abokan gaban, inda…

Read More