Labarin dake shigo mana daga jihar Kaduna na bayyana cewar wasu da ake zargi ‘yan bindiga ne ?auke da muggan makamai sun kashe mutum hudu a wani kauye ciki har da wani sabon malami a karamar hukumar Kajuru dake jihar ta Kaduna.
Harin ya yi sanadin rayuka uku ciki har da wani shugaban matasa a daren ranar Lahadi. Mazaunin garin ya yi ?arin haske kan harin Within Nigeria ta tattaro cewa a harin na biyu a Tudun Mare ne aka kashe wani malami mai suna Elisha Arziki.
Wani mazaunin garin mai suna Benjamin, ya ce: “Yan bindigan sun kashe shugaban matasan da wasu mazauna kauyen biyu lokacin da suka kawo hari a ranar Lahadi. An birne su a ranar Lahadi. Yan bindigan kuma sun kashe wani malami a kauyen Tudun Mare a daren ranar Litinin.”
Kakakin yan sandan jihar Kaduna, DSP Mohammed Jalige ya yi alkawarin zai kira Wakilinmu ya bada karin bayani amma bai kira ba har lokacin hada wannan rahoton.
