Ba Gaskiya Bane Cewa Mun Katse Layin Wayoyi A Katsina – NCC

Hukumar sadarwa ta NCC a Najeriya ta karyata rahotanni da ake ya?awa a shafukan sada zumunta cewa ta katse layukan wayoyin sadarwa a jihar Katsina.

Shugaban hukumar a wata sanarwa da ya fitar, Farfesa Umar D. Danbatta wanda ya zanta da gwamnatin jihar ya ce labaran boge ake ya?awa.

NCC ya ce sanarwar da aka fitar kan Zamfara shi ne mutane suka jirkita ta da alakanta sanarwar da Katsina.

Tun a sanyin safiyar yau sanarwar ke ta yawo a shafukan sada zumunta cewa an toshe layukan sadarwa a Katsina da jihohi makwabta.Article share tools

Related posts

Leave a Comment