Talauta Kaduna Da Bashi: An Yi Zanga-Zangar Neman Titsiye El-Rufa’i

IMG 20230808 WA0052(1)

Rahotannin dake shigo mana daga Jihar Kaduna na bayyana cewa Gamayyar kungiyoyin wanzar da zaman lafiya da fafutukar kwato haqqin alumma ta Coalition of Civil Society Organization a karkashin Shugabanta Engr Aminu Idris ta gudanar da zanga-zanga.

An gudanar da zanga-zangar ne domin bayyana korafi akan zargin da ake yiwa gwamnatin El-rufai na tara bashi ba tare da aiwatar da abin da ya kamata ba.

Zanga-zangar wacce ta gudana a garin Kaduna ta kunshi mambobin kungiyoyi 27 wadanda suka bukaci da ayi gaggawar gudanår da bincike akan lamarin.

An shiga cikin wani yanayi a Kaduna tun bayan korafin da Gwamnan jihar Uba Sani ya yi na zargin gwamnatin El Rufai da cin bashin da ya kai jihar ga shiga cikin mawuyacin hali.

Related posts

Leave a Comment