Rahotannin dake shigo mana daga Jihar Kaduna na bayyana cewa Gamayyar kungiyoyin wanzar da zaman lafiya da fafutukar kwato haqqin alumma ta Coalition of Civil Society Organization a karkashin Shugabanta Engr Aminu Idris ta gudanar da zanga-zanga.
An gudanar da zanga-zangar ne domin bayyana korafi akan zargin da ake yiwa gwamnatin El-rufai na tara bashi ba tare da aiwatar da abin da ya kamata ba.
Zanga-zangar wacce ta gudana a garin Kaduna ta kunshi mambobin kungiyoyi 27 wadanda suka bukaci da ayi gaggawar gudanår da bincike akan lamarin.
An shiga cikin wani yanayi a Kaduna tun bayan korafin da Gwamnan jihar Uba Sani ya yi na zargin gwamnatin El Rufai da cin bashin da ya kai jihar ga shiga cikin mawuyacin hali.
