Hajiya Halima Iliya, shugabar shirin samar da ku?a?en bayar da kariya ga makarantu na ?asa, ta ce hukumar ta tattara bayanai da za su taimaka wajen kai wa makarantun ?auki.
A shekarar 2014 ne aka kafa hukumar bayan sace ?aruruwan ?aliban makarantar Chibok da ke jihar Borno a arewa-maso-gabashin ?asar.
Jihohin da wasu makarantunsu ke cikin ha?arin sun ha?a da Adamawa, Bauchi, Borno, Benue, Yobe, Katsina, Kebbi, Sokoto, Filato, Zamfara da birinin Abuja. A cewar hukumar.
A ranar Alhamis da ya wuce ne ?anbindiga suka sace ?alibai 270 na makarantun firamare da sakandire a ?auyen Kuriga da ke jihar Kaduna.
Haka kuma a ranar Asabar da ta wuce ne wasu ?anbindigar suka sace ?aliban makarantar tsangaya kimanin 15 a ?aramar hukumar Gada a jihar Sokoto.
Sace-sacen sun biyo bayan sace wasu ?aruruwan ?angudun hijira a Ngala da ke jihar Borno da ake zargin ?anBoko Haram da aikatawa.
Iyaye da ?an’uwan ?alibai da sauran wa?anda aka sacen na ci-gaba da ro?on gwamnati ta ku?utar da su.
