Kaduna: Kungiyar ‘Yan Jarida Za Ta Kaurace Wa Taron PDP

Kungiyar ‘yan Jarida ta ?asa reshen Jihar Kaduna ta yi kira da babbar murya ga jam’iyyar PDP da ta gargadi jami’in ya?a labarai na jam’iyyar a jihar Kaduna Katoh Alberah a ?o?arin da yake yi na raba kawunan ‘yan Jarida a jihar.

Kiran ya biyo bayan matakin da jami’in ya?a labaran ya ?auka na za?ar wasu ‘yan Jarida a matsayin wadanda za su yi rahoto a za?en fidda gwani na jam’iyyar da ke gudana a Kaduna da yin watsi da wasu ‘yan Jaridar.

Kungiyar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da suka fitar ranar Laraba a Kaduna a taron karshen wata da kungiyar da ya gudana a Kaduna.

A cikin takardar bayan taron wadda ta samu sanya hannun Usman Sani ta bayyana matakin da Mista Katoh Alberah ke dauka a matsayin wani yunkuri na haifar da rarrabuwar kawuna tsakanin ‘yan Jarida a jihar.

Sanarwar ta bayyana jami’in ya?a labaran a matsayin Mutum mai ?agawa da nuna girman kai ga ‘yan Jarida a jihar.

Kungiyar ta shawarci ‘yan Jarida a jihar da su cigaba da gudanar da ayyukan su cikin tsari da ha?in kai da kauce wa dukkanin wani abu da zai kawo sa?ani a tsakanin su.

“Matu?ar Mista Katoh Alberah zai cigaba da yin hakan babu shakka ?ungiyar ba ta da wani za?i wanda ya wuce ta ?auracewa ?aukan labaran jam’iyyar PDP a Jihar.

Daga ?arshe ?ungiyar ta yi Allah wadai da cin zarafin da wasu jami’an tsaro suka yi wa ‘yan Jarida a yayin taron da Jam’iyyar PDP ta gudanar kwanan nan.

Related posts

Leave a Comment