Cin Hanci Da Rashawa Ya Fi Muni A Mulkin Buhari Fiye Da Mulkina- Babangida

Tsohon shugaban mulkin sojan Najeriya Ibrahim Babangida ya ce ya fi Shugaba Muhamamdu Buhari da sauran shugabannin dimokuradiyar ?asar ya?i da rashawa.

Tsohon sugaban ya shaida hakan ne a lokacin wata hira ta musamman da tashar ARISE TV a wannan Juma’ar.

Ya kuma ce mutanen da suka yi aiki a ?arkashinsa mutanen kirki ne sama da wanda ake gani yanzu haka a mulki.

Shugaban na mulkin soja ya ce yayinda ya ya?i tsohon gwamnan mulkin soja da ya wawushe N313,000, mutanen da suka sace biliyoyi na tafiya a yanzu cikin ?anci.

Da aka tambaye shi cewa ko ya amince cewa rashawa ta yawaita a lokacin mulkinsa, IBB ya mayar da martani cewa, “ba abu ne da za a iya kwatantawa da wanda ake gani yanzu a zahiri ba.

“Daga abin da na karanta, da kuma sharhi, ina ganin mu tsarkakakku ne idan aka kwatanta da abin da ke faruwa a yanzu karkashin mulkin dimokuradiya.

“Na kori gwamna kan sata da almubazaranci kan kasa da N313,000 amma a yau, mutanen da suka wawushe bilyoyi har maganarsu na kotu na tafiya hankali kwance a titi. Don haka wane ne ya fi ya?ar rashawa?”

IBB yana da kyakyawan ala?a da shugaba Buhari, da ?aura alhakin sa?anin da ake ganin akwai tsakaninsu kan kofofin yada labarai

Related posts

Leave a Comment