Babbake Dazukan Arewa Ne Maganin ‘Yan Bindiga – El Rufa’i

Rahotanni daga Jihar Kaduna na bayyana cewar Gwamnan Jihar Malam Nasir El-Rufai ya bayar da shawarar a ?ona dazukan arewa domin ?akkabe ?arayin daji da suka addabi yankin.

“Na sha fa?a cewa, abin da ya kamata shi ne a ?ona dajin, a kashe su gaba ?aya, daga baya mu sake shuka bishiyoyi,” kamar yadda gwamna El-Rufai ya shaidawa kafar Arise TV a wata hira ta musamman.

Ya ?ara da cewa ?ona dajin ne kawai mafita duk da matakin zai shafi wa?anda ba su ji ba su gani ba.

“Ya fi a kakkabe su a dawo da zaman lafiya mutane su koma noma,” in ji shi.

Ya ce yadda ake tunkararsu ba zai kawo ?arshen matsalar ba – “domin idan an kore su daga Sokoto, za su tsere su tsallaka Kebbi.”

“Abin da za a yi kawai a yi masu ruwan wuta ta sama da ?asa a dukkanin jihohi shida na arewa maso yammaci da Neja.”

“Idan aka yi haka ina ganin cikin makwanni ana iya maganin matsalar ”

Related posts

Leave a Comment