An Dakatar Da Rasha Daga Kwamitin Kare Hakkin Dan Adam

Babban zauren Majalisar ?inkin Duniya ya kada kuri’ar dakatar da Rasha daga hukumar da ke kare hakkin dan Adam yayin wani zama da aka yi a birnin New York.

Matakin ya biyo bayan tuhumar da ake ma Rasha cewa sojojinta na aikata laifukan yaki a Ukraine.

Kafin a akada kuri’a, jakadan Ukraine a Majalisar Dinkin Duniya SErgiy Kyslytsya ya tuhumi Rasha da aikata munanan laifuka – musamman bayan kashe-kashen da ake tuhumar Rashar da aikatawa a garin BUcha.

Wakilin Rasha Gennady Kuzmin ya yi tir da kuri’ar, sannan kuma wasu kasashe, ciki har da Koriya ta Arewa da Syria sun mara ma sa baya.

Related posts

Leave a Comment