Adamawa: Lamido Ya Bukaci Iyaye Su Ilimantar Da ‘Ya’yansu Al-Kur’ani

An kira yi al’umma Musulmi da su mai da hankali wajen ba ‘ya’yan su ilimin Al-qur ani mai girma domin samar musu nagartacecen ilimin addinin musulunci.

Mai martaba Lamidon Adamawa Dr Muhammadu Barkindo Aliyu Mustafa ne yayi wannŕn kira a lokacin da yake jawabi a wurin bu?e gasar karatun Al-qur ani mai girma na kasa wanda kungiyar shirya gasar Alqur’ani na ?alibai Mata zalla (RABIDA) ta shirya a Yola.

Lamido wanda hakimim cikin garin Yola kuma Cika Soron Adamawa wato Muhammed Ahmed Mustafa ya wakillta yace ba yara ilimin addini tun suna kanana yana da matukar muhimmanci wanda a cewarsa hakan zai taimaka wajen cigaban addinin musulunci yadda ya kamata.

Lamido ya kuma shawarci Al’umma Musulmai da su kasance masu sanya tsoron Allah madaukakin sarki a zukatansu a koda yaushe domin samun tsira ranan gobe kiyama.

Shima tun da farko a jawabinsa shugaban kwamitin shirya gasar kuma shugaban majalisar addinin musulunci a jihar Adamawa Malam Gambo Jika ya nuna farin cikinsŕ dangane irin goyon baya da Al’umma Musulmai suka bayar domin ganin an gudanar da gasar cikin lumana.

A nata jawabi Amiran Rabida a jihar Adamawa kiran iyaye mata tayi da su mai da hankali wajen ba yaransu tarbiya ta gari musammanma mata kasancewarsu iyayen Al’umma.

Za a dauki a kalla mako daya ana gudanar da gasan wanda zai gudana a makaranta kwalejin ilimi ta tarayya dake Yola, wanda kuma ana saran daukacin jihohi talatin da shida harda birnin tarayya Abuja zasu halarci gasar karatun Al Qurani mai girma.

Related posts

Leave a Comment