Adamawa: An Shawarci ‘Yan Kasuwa Da Shiga Harkar Noma

An bukaci yan kasuwa da masu kamfanoni su shuga adama dasu a cikin harkokin noma domin bunkasa harkan noma dama wadatar da kasa da abinci yadda yakamata.

Alhaji Adamu Jingi wanda akafisani da mai hangene ya baiyana haka a zantawarsa da muryar yanci a yola fadar gwamnatin jahar Adamawa.

Alhaji Adamu Jingi yace mai makon maida hankali a bangaren ginai ginai kamata yayi yan kasuwa dama kamfanoni su maida hankali wajen bunkasa noma wanda a cewarsa hakan zai taimaka wajen samun saukin kayakin abinci a fadin Najeriya.

Alhaji Adamu ya kuma jirayi gwamnatin tarayya data kara himma wajen tallafawa kananan manoma musammanma wadanda ke zaune a yankunan karkara.

Ya kuma shwarci matasa da auma kar su bari a barsu a baya sukasance masu maida hankali wajen rungumar harkokin noma wanda hakan zai basu damar dogaro da Kansu.

Harwayau Adamu Jingi ya shawarci manoma da su kasance masu neman ilimin harkokin noma a koda yaushe domin samun cigaba a bangaren noma yadda ya kamata.

Related posts

Leave a Comment