2023: El Rufa’i Zai Yi Gudun Hijira Bayan Mika Mulki – Babawo

Rahoton dake shigo mana daga Jihar Kaduna na bayyana cewar ‘yan majalissar jihar sun roki jagoran APC wanda ke neman takarar shugaban kasa, Tinubu cewa ya zabi gwamna El Rufa’i a matsayin mataimakinsa.

A ranar Alhamis Tinubu ya ziyarci Kaduna domin ganawa da wakilau 66 na jihar cewa su zabe shi a zaben fidda gwani da za’ayi.

Inda dan majalisa dake wakiltar ?aramar hukumar Sabon Gari Garba Babawo ya bayyana cewa suna rokon wata alfarma a wurin Tinubu wacce basu sanar da El Rufa’i ba domin ba zai amince ba.

Cewa don Allah ya zabi gwamna El Rufa’i a matsayin mataimakin shi a zaben shekarar 2023 saboda su san cewa gwamna kasar waje zai tafi da zarar ya sauka a mulki, amma su suna so ya cigaba da yiwa Najeriya hidima.

Related posts

Leave a Comment