Za Mu Shawo Kan Matsalar ?arancin Fetur Nan Da ‘Yan Kwanaki – NNPC

Shugaban Kamfanin mai na Najeriya, NNPCL, Mele Kyari ya bayyana fatan cewa layuka a gidajen sayar da mai a fadin kasar zai zama tarihi nan da kwana biyu masu zuwa.

Kyari ya shaida hakan ne a hirarsa da gidan Talabijin na Channels inda ya ce halin da aka shiga ba mai dorewa bane.

A cewarsa, baya tunanin dogayen layukan da ake kafawa zai kai har zuwa ranar Asabar.

Ya bayyana cewa akwai sama da lita miliyan 810 na man fetur a depo-depo da tankoki da kuma gidajen man da ke fadin Najeriya.

A ranar Litinin ne yayin jawabinsa bayan shan rantsuwar kama aiki, sabon shugaban kasa, Bola Tinubu ya ce zamanin biyan tallafin mai ya zo karshe, matakin da ya haifar da tashin farashin man fetur a sassan kasar.

Sai dai wakilin BBC ya ce an samu raguwar layukan mai a Abuja, babban birnin Najeriya duk da a wasu jihohin, lamarin bai janye ba.

Related posts

Leave a Comment