Soke Jam’iyyu: Za Mu Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu – INEC

Shugaban hukumar za?e Farfesa Mahmud Yakubu ya ce INEC za ta bi duk wani umarnin kotu game da sokewa ko yi wa jam’iyyun siyasa rajista a ?asar.

Farfesa Yakubu ya bayyana hakan ne a yau Asabar yayin wani taron ?ara wa juna sani da ke gudana yanzu haka a Abuja game da babban za?en ?asar da ke tafe a 2023.

Tun a watan Fabarairu na 2020 ne INEC ta soke jam’iyyun siyasa 74 a Najeriya, abin da ya hana su shiga duk wani za?e da za a gudanar a ?asar.

Da aka tambaye shi game da dalilin da ya sa INEC ta soke rajistar jam’iyyar Youth Party (YP) duk da umarnin kotu, shugaban hukumar ya ce har yanzu batun yana kotu.

Related posts

Leave a Comment