Najeriya ta samu gurbin shiga gasar Kofin Afirka ta 2021 bayan Lesotho da Sierra Leone sun buga canjaras a wasansu a rukunin L.
Sakamakon wasan ne ya bai wa tawagar ta Super Eagles damar shiga gasar tun kafin take wasanta da Benin a yau Asabar.
Najeriya ta doke Benin 0-1 a wasan da suka take da ?arfe 5:00, abin da ya sa ta samu maki 11, Benin na da bakwai, Sierra Leone na da hu?u sai kuma Lesotho mai uku a rukunin.
?asashen da suka ?are a mataki na ?aya da na biyu ne za su halarci gasar a Kamaru, wadda ?asashe guda 24 za su fafata a karo na 33.
Benin da Najeriya ne suka samu gurbin shiga gasar daga rukunin na L.
Tawagar Super Eagles ta lashe kofin gasar sau uku a tarihi.
Sauran ?asashen da suka fito zuwa yanzu:
- Algeria
- Burkina Faso
- Kamaru
- Comoros
- Egypt
- Equatorial Guinea
- Gabon
- Gambia
- Ghana
- Guinea
- Ivory Coast
- Mali
- Morocco,
- Senegal
- Tunisia
- Zimbabwe
