?ungiyar cigaban Matasan Arewa wato Arewa Youth Forum (AYF) a takaice, ta yi kira da babbar murya ga Shugaban ?asa Buhari da ya yi gaggawar ?aukar mataki da?ile rikicin da ya kunno a sashin Kudancin kasar na kisan ‘yan Arewa, domin kawar da yiwuwar faruwar ya?in basasa a ?asar.
Kungiyar ta bayyana hakan ne a cikin wata takardar sanarwa dake dauke da sa hannun Shugaban ?ungiyar Alhaji Gambo Ibrahim Gujungu, kuma aka rarraba ta ga manema labarai a Kaduna.
Matasan sun bayyana cewar ba ?aramin kuskure ba ne furucin da Gwamnan jihar Ondo Rotimi Akeredolu ya yi ba na bada umarni korar Fulani daga jihar, wanda tabbas wannan babu abin da zai haifar da gagarumar matsala a ?asar.
Matasan sun kara da cewar babu wata ?asa da za ta iya samun nasara a hali na rashin tsaro, saboda haka alhakin gwamnatin l ne ta kare dukiya da rayukan jama’ar da suka zabe ta.
“Halin da ?asa ke ciki nauyi ne da ya rataya a kafadun gwamnatoci baki daya na tarayya da jihohi, ba al’amari ba ne da za’a ?ora shi a bangare guda, bisa ga haka ya zama tilas e ayi dukkanin mai yiwuwa wajen magance matsalar.
“Muna kira da babbar murya ga gwamnati da cewar lallai a tabbatar an kama dukkanin wa?anda ke da hannu a rura wutar rikicin nan, a tabbatar a hukunta su domin rashin aikata hakan zake haifar da barazana ga al’umma baki ?aya”.
Kungiyar ta kuma yaba gami da jinjina ga shugaban ?asa Buhari na amsa kiran ‘yan Najeriya da ya yi na canza shugabanni tsaro, lallai wannan abin a yaba ne.
Sannan Matasan na Arewa sun kuma yaba matakan da sabbin shugabannin tsaron ke ?auka na jajircewa wajen yaki da kawar da matsalar tsaro wadda ta ke addabar sashin Arewacin Najeriya.
