Karancin Kudi: Karuwai Sun Koka Kan Rashin Ciniki A Abuja

Wasu karuwai a babban birnin tarayya, FCT, Abuja sun koka kan rashin ciniki a kasuwancinsu sakamakon karancin tsabar ku?i a hannun kwastomomi.

Wasu daga cikinsu da su ka zanta da Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya a Abuja a yau Lahadi sun ce ?arancin tsabar ku?i na zama barazana kuma ya gurgunta kasuwancinsu.

Sun ce duk da cewa manufar musanya kudi abin yabawa ne, amma yadda ake aiwatar da ita a halin yanzu kalubale ne ga kasuwancinsu.

Karuwan sun ce abokan cinikin su sun ragu sosai saboda halin da ake ciki na rashin tsabar ku?i.

Sun bayyana yanayin a matsayin abin takaici da tafiyar hawainiya ga kasuwancin su.

Related posts

Leave a Comment