Kano: Kotu Ta Kwace Takarar Gwamna Daga Hannun Mohammed Abacha

Rahoton dake shigo mana daga jihar Kano na bayyana cewar Kotun daukaka kara da ke zama a Kano ta soke hukuncin babban kotu da ta bayyana Muhammad Abacha matsayin ‘dan takarar gwamnan jihar Kano karkashin jam’iyyar PDP.

Kotun daukaka karar ta yi umarnin cewa, Sadiq Wali, wanda a baya hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, INEC, ta ayyana shi matsayin ‘dan takara, shi ne sahihin ‘dan takarar.

A hukuncin da alkalai uku suka yanke, Mai Shari’a Usman Musale, kotun ta yanke hukuncin cewa a bayyane yake NEC din jam’iyyar za ta iya zaben fidda gwanin jam’iyyar kuma tunda Abacha bai yi zaben da NEC ta samar da Wali ba, bashi da hurumin kalubalantar zaben.

Related posts

Leave a Comment