Kaduna: An Tarwatsa Shirin ‘Yan Bindiga Na Hada Bama-Bamai

Rahotannin dake shigo mana daga jihar Kaduna na bayyana cewar Jami’an tsaro sun kama buhunan takin zamani 27 da ake zargin ‘yan bindiga na shirin ha?a abubuwan fashewa da su a Jihar.

Sanarwar da Kwamashinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Kaduna Samuel Aruwan ya fitar ta ce dakaru sun far wa sansanin jagoran ‘yan fashi Lawal Kwalba bayan sun samu bayanan sirri a yankin Dende na ?aramar Hukumar Chikun.

“Dakarun sun gano batiri-batiri da kuma buhuhunan takin zamani 27…wa?anda ake kyautata zaton za su ha?a abubuwan fashewa da su ganin irin ala?arsu da ‘yan ta’adda (Boko Haram),” a cewar Mista Aruwan.

Kazalika, jami’an tsaro sun gano babur ?aya da wayar salula biyu a sansanin bayan ‘yan bindigar sun tsere kafin dakarun su cim musu.

Haka nan, an kama wasu mutane a yankin bayan jami’an tsaron sun ci gaba da bin sawun su kuma ana ci gaba da bincike kan su, a cewarsa.

Related posts

Leave a Comment