Rahotanni daga Jihar Kaduna na bayyana cewar Shugaban hukumar zaben jihar Kaduna (SIECOM) Dr. Saratu Dikko Audu ta bayyana ?age zaben kananan hukumomin jihar zuwa ranar 4 ga watan Satumban 2021.
Ta bayyana hakan ne a hedkwatar hukumar a wani taro da suka yi ranar Litinin a Kaduna kamar yadda Jaridar Daily Trust ta ruwaito.
An ruwaito yadda aka tsara zaben shugabannin kananan hukumomi 23 da kansiloli ya zama ranar 5 ga watan Yuni 2021 kafin a dage zuwa 14 ga watan Augusta, sannan zuwa 4 ga watan Satumba.
