Harkar Fim Har Yanzu Ina Jan Zarena Bai Tsinke Ba – Abba Al-Mustapha


Fitaccen Jarumi a Masana’antar shirya fina-finai ta Kannywwod Abba Almustapha yace har yanzu ba a daina yayin sa ba, a cikin Masarautar kannywwod, duk da ba Koda yaushe ake ganin sa a cikin harkar fim din ba.

Jarumin ya bayyana Hakan ne a lokacin tattaunawar su da Jaridar Dimukaradiyya dangane da masu cewar an daina yayin sa a harkar fim.

Sai yace “Gaskiya ba daina yayina aka yi ba domin mun kafa tarihi a Masana’antar da baza a taba manta damu ba”

Inda ya Kara da cewar “Kowa ya san irin rawar da muka taka a baya, Kuma har yanzu idan na samu lokaci na fito a fim zaka ga yadda Jama’a suke yabawa don haka mu sai godiya ga Allah, domin mun bar tarihin da a harkar fim da ba za a daina yayin mu ba.”

Dangane da rashin ganin sa kuwa a cikin shirin fim, cewa ya yi “To ka San ita harkar rayuwa Kullum ci gaba a ke nema, don haka shekaru uku zuwa hudu da suka wuce na koma karatu a B U K in da na kammala Digiri sannan Kuma na ci gaba har ma a yanzu na Kai matakin karshe Ina daf da kammalawa, Amma dai duk da haka in na samu lokaci na Kan Dan fitowa a fim kamar yadda masu kallo su ke gani.”

Daga karshe ya yi wa masoyan sa dasu ke yi bibiyarsa tare da kara masa kwarin gwiwa masa fatan alheri.

Related posts

Leave a Comment