Shugaban kungiyar gwamnonin APC kuma gwamnan jihar Kebbi, Abubakar Atiku Bagudu ya yi watsi da ikirarin cewa wasu gwamnonin jam’iyyar na tattaunawa da dan takarar shugaban kasa, jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar.
Bagudu ya ce Gwamnonin APC ba sa aiki da PDP a kan burin dan takarar shugaban kasa na jam’iyya mai mulki, Bola Tinubu.
Ya bayyana hakan ne a yayin taron yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC a Kano .
Bagudu ya ba da tabbacin cewa gwamnonin APC na bayan burin Tinubu na zama shugaban kasa.
A cewar Bagudu: “Dukkan gwamnoninmu suna goyon bayan takarar Tinubu.
“Ikirarin da wasu ke cewa wasu gwamnonin APC na tattaunawa da ‘yan adawa karya ne. Dukkan gwamnoninmu suna goyon bayan takarar Tinubu
Kalaman na sa sun zo ne lokacin da Gwamna Nyesom Wike ya yi zargin cewa wasu gwamnonin APC na aiki da Atiku.
