Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ba haka kawai gabaga?i ake fitowa a ayyana cewa ‘yan bindiga su ma ‘yan ta’adda ne ba.
Ministan Harkokin Tsaro Bashir Magashi ne ya bayyana haka, tare da cewa akwai matakan da ake bi, kuma ko an bi su ?in, to sai an tabbatar da kammaluwar su sannan za a ayyana cewa ‘yan bindiga ma ‘yan ta’adda ne.
Magashi ya yi wannan furuci a lokacin da ya kai ziyarar gani da idon irin ci gaban da ake samu a filin dagar ya?i da Boko Haram a Barno.
Ya na tare da rakiyar Babban Hafsan Tsaron ?asa, Lucky Iraboh da sauran manyan hafsoshin ?asa, ruwa da na sama.
Ya kuma gaba da manyan kwamandojin ya?i na Arewa maso Gabas, wato ‘Threater Commanders’, tare da nuna gamsuwa da irin ?o?arin su da nasarorin da ake kan samu a yanzu.
Magashi ya yi wannan bayani ne biyo bayan tambayoyin da manema labarai su ka yi masa a Maiduguri, dangane da tsaikon da ake samu wajen ?in kiran ‘yan bindiga da suna ‘yan ta’adda da Gwamnatin Tarayya ta ?i yi.
