Buhari Ya Yi Rawar Gani A Fannin Tsaro – Ban Ki-moon

Rahotanni daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar tsohon Sakataren Majalisar ?inkin Duniya Ban Ki-moon ya yaba gami da jinjina wa kokarin shugaba Buhari ta fuskar samar da tsaro.

A cikin wata takardar sanarwar da mai bai wa shugaban shawara kan yada labarai Malam Garba Shehu ya sanya wa hannu, ta ce Moon ya jinjina wa Shugaba Buhari game da shawo kan matsalar tsaro da kasar ke fama da ita.

Garba Shehu ya ce shugaban ya gode wa tsohon Magatakardar Majalisar Dinkin Duniyar kan gudunmawar da ya bai wa Najeriya a lokacin da yake kan aiki.

Mista Moon ya kuma gode wa shugaban ma’aikatan fadar shugaban Najeriya Farfesa Ibrahim Gambari da ya taba aiki karkashin sa, da kuma Mataimakiyar Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Hajiya Amina Muhammad, wadanda ya ce shekarun da suka yi aiki tare masu muhimmanci ne da kokarin kawo ci gaba a Najeriya.

Related posts

Leave a Comment