Borno: Zulum Ya Hana Sanya Sunan Sa Jikin Ayyukan Da Ya Yi

Rahotanni daga Maiduguri babban birnin jihar Borno na bayyana cewar Gwamnan jihar Farfesa Babagana Umara Zulum ya yi watsi da sunansa da aka saka a ginin wasu ?akunan kwanan ?alibai a Kwalejin fasaha ta Ramat a Maiduguri na gwamnatin jihar.

Zulum ya yi watsi da karamcin ne lokacin da yake ?addamar da ginin da ma’aikatar ilimi ta gyara.

A sanarwar da gwamnatin Borno ta fitar, Zulum ya ce “Ba zan yarda a saka sunana a wani aikin gwamnati ba, a lokacin da nake kan mulki. Ya kamata ko za a yi sai na gama wa’adi na.”

Maimakon sunansa, gwamna Zulum ya bu?aci a sauya zuwa “?akin kwanan ?alibai maza.”

Related posts

Leave a Comment