Rahoton dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Honorabul Gudaji Kazaure ya bayyana mutane 7 da yace dole sai shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kamasu idan yana son mulkinsa ya tafi daidai
Tsohon dan majalisar daga jihar Jigawa, Gudaji Kazaure ya bayyanawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu cewa, akwai mutanen da idan bai kamasu ba, kasarnan ba zata zauna daidai ba.
Kazaure ya bayyana hakane a cikin wani bidiyo yayin wata ganawa da shugaban gidan Rediyon Berkete Family Ahmad Isa yayi dashi.
Yace mutanen sune:
Godwin Emefiele
Abdulrashid Bawa
Wadannan mutanen duka suna hannu a yanzu an kamasu.
Sauran sune:
Yace kuma ya kamata a gayyaci tsohon shugaban EFCC, Ibrahim Magu ya bayyana ahinda ya bari a ofis wanda Abdulrashid Bawa ya tarar.
Sai kuma tsohon ministan shari’a, Abubakar Malami
Tunde Buhari
Shugaban NNPCL, Mele Kolo Kyari.
Shugaban FIRS, Muhammad Nnami
Tsohuwar shugabar hukumar Port Authority, Hadiza Bala.
Dr. Bashir Jamo shugaban Nimasa.
Muhammad Bello Koko, shugaban NPA na yanzu
Yace da kuma duka mataimakan gwamnan babban bankin Najariya, Godwin Emefiele ya kamata a kamosu a tambayesu abinda suka sani.
