Najeriya Ta Samu Shiga Gasar Nahiyar Afirka

Super Eagles

Najeriya ta samu gurbin shiga gasar Kofin Afirka ta 2021 bayan Lesotho da Sierra Leone sun buga canjaras a wasansu a rukunin L.

Sakamakon wasan ne ya bai wa tawagar ta Super Eagles damar shiga gasar tun kafin take wasanta da Benin a yau Asabar.

Najeriya ta doke Benin 0-1 a wasan da suka take da ?arfe 5:00, abin da ya sa ta samu maki 11, Benin na da bakwai, Sierra Leone na da hu?u sai kuma Lesotho mai uku a rukunin.

?asashen da suka ?are a mataki na ?aya da na biyu ne za su halarci gasar a Kamaru, wadda ?asashe guda 24 za su fafata a karo na 33.

Benin da Najeriya ne suka samu gurbin shiga gasar daga rukunin na L.

Tawagar Super Eagles ta lashe kofin gasar sau uku a tarihi.

Sauran ?asashen da suka fito zuwa yanzu:

  • Algeria
  • Burkina Faso
  • Kamaru
  • Comoros
  • Egypt
  • Equatorial Guinea
  • Gabon
  • Gambia
  • Ghana
  • Guinea
  • Ivory Coast
  • Mali
  • Morocco,
  • Senegal
  • Tunisia
  • Zimbabwe

Related posts

Leave a Comment