Shugaban Kungiyar Kiristocin Nijeria, CAN, Rev. Samson Ayokunle, ya yi kira ga ‘yan Nijeriya musamman ma ‘yan Kudancin Kasar da su fitar da Shugaban kasa kirista wanda zai ja ragamar Shugabanci a 2023.
Ayokunle ya bayyana haka ne a liyafar zagayowar ranar wani dakin taron hukumar cocin Christ Revival karo na 53 a Ibadan babban birnin Jihar Oyo.
“Ina so na yi kira ga dukkan Kiristocin dake dakin taron nan kuma na fada wa sauran ‘yan Nijeriya cewa kuna kuka akan gurbataccen Shugabanci a Najeriya lokaci yayi da zaku canza gurbatattun Shugabannin ku da kuri’arku.
“Kuna cewa baku son rashin shugabanci nagari a Nijeriya, muna neman mutane kwararru wadanda zasu jagoranci Nijeriya ta yadda mutane zasu ji dadi su nuna godiyarsu.
“Wannan wata dama ce garemu daga kuri’unku. Duk wanda bai amshi katin zaben shi ba to ya garzaya ya karba. Idan kana da matsala wajen karbar naka to ka fada mana.
“Ba zaka zauna a gida ba kuma ka tsammaci Shugabanci nagari ba tare da ka zabi nagari ba. zaben shugaba nagari yana hannunka. ka amshi katin zaben ka akan lokaci.
Ba za mu sake bari mutanen banza su mulke mu ba “Mutanen banza ba zasu kara mulkar Nijeriya ba, kar ka zabi mutum saboda yana da kudi ko ya shahara, ka zabi wanda yake da tsoron Allah a cikin rayuwarshi.
“Yan Arewa sun mulke mu na tsawon shekaru takwas kuma dukkansu musulmai ne. Saboda haka yanzu lokacin kirista ne da zai hau shima yayi shekaru takwas, saboda haka Allah yakeso, ya halicce mu kowa dai dai a Nijeriya.
“Mu kusan miliyan 200 ne a Nijeriya; kiristoci miliyan 100, musulmai ma miliyan 100. “Ba zaka fada min cewa bayan shekaru 8 na mulkin dan Arewa musulmi, ba zaka samu kirista daya kwararre ba daga kudu cikin kiristoci miliyan 100 da zai iya hawa mulki ba na wasu shekaru takwas.
