Buhari Ya Dawo Najeriya Daga Birnin Landan

Labarin dake shigo mana daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar bayan shafe akalla kwanaki 12 a kasar Burtaniya, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dawo Najeriya.

Shugaban ya tafi birnin Landan kusan makwanni biyu da suka gabata domin ganawa da masu duba lafiyarsa kamar yadda ya saba a duk shekara.

Shugaban ya dawo gida a ranar Juma’a, inda ya samu tarbar wasu daga cikin jiga-jigan gwamnati a fadarsa da ke Abuja.

Rahotanni sun bayyana cewar jirgin shugaban kasan ya sauka a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja ne da misalin karfe 7.09 na dare.

Related posts

Leave a Comment