2023: Ba Na Goyon Bayan Kowa – Obasanjo

Rahotannin dake shigo mana daga Minna babban birnin Jihar Neja na bayyana cewar tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo ya ce babu ?an takarar shugaban ?asa da yake mara wa baya a babban za?en dake tafe na na 2023.

Da yake magana a Minna, babban birnin Jihar Neja yayin ziyarar da ya kai wa Tsohon Shugaban ?asa Badamasi Babangida ranar Lahadi, Obasanjo ya ce Najeriya ce a gabansa ba wani ?an takara ba.

“Ba ni da ?an takara, ?asa ce a gabana,” in ji shi. “Na zo ziyarar ?an uwana da ya yi ‘yar rashin lafiya, wanda na so na yi hakan tun yana Landan amma sai ya koma gida a ranar da na isa Landan ?in.”

A makon da ya gabata, an ga Obasanjo a birnin Landan na ganawa da ?an takarar jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, da sauran ‘yan siyasa. Kafin haka, ?an takarar APC, Bola Tinubu, ya ziyarce shi a birnin Abeokuta na Jihar Ogun.

Related posts

Leave a Comment