Za A Kara Farashin Kudin Burodi A Najeriya

?ungiyar masu gidajen burodi a Najeriya ta ce za ta ?ara farashin burodi da kashi 15 cikin ?ari daga ranar 24 ga watan Juli.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, bayan kammala taron shugabanninta na ?asa, ?ungiyar ta ‘Association of Master Bakers and Caterers of Nigeria’ ta ce ta ?auki matakin ne bayan la’akari da nunnukawar farashin kayan aiki.

Sanarwar wadda ta samu sa hannun shugaban ?ungiyar na ?asa, Alhaji Mansur Umar ta ce tashin farashin ya biyo bayan cire tallafin man fetur da gwamnatin Tarayya ta yi.

A ranar 29 ga watan Mayun 2023 ne shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya sanar da cire tallafin man fetur a cikin jawabinsa na kar?ar mulki.

Lamarin ya haifar da tashin litar man fetur daga kimanin naira 200 zuwa sama da naira 500 a fa?in ?asar, wani abu da ya haifar da tashin farashin sufuri da kayan masarufi.

?ungiyar ta ce abubuwan da take amfani da su wajen gudanar da sana’ar, wa?anda suka ha?a da man fetur, da gas, da fulawa, da suga da sauran su duk sun yi tashin gwauron zabi.

Haka nan ?ungiyar ta koka kan yadda hukumomi daban-daban a ?asar ke kar?ar haraji, kala-kala, wani abu da ke ?ara saka masu gidajen burodin cikin matsi.

Kan haka ne ta ce “An umurci dukkanin shugabannin ?ungiyar na yanki su tabbatar cewa ?a?an ?ungiyar sun bi wannan umarni, har sai idan sun samu wani sabon umarnin daga uwar ?ungiyar ta ?asa.”

Related posts

Leave a Comment