Labarin dake shigo mana yanzu haka daga Gusau babban birnin Jihar Zamfara na bayyana cewa kwanaki hu?u bayan kai wani hari da ya yi sanadin mutuwar mutum a?alla 12 a ?aramar hukumar Maru cikin jihar har yanzu ‘yan bindiga sun hana a je a ?auko gawarwakin don yi musu jana’iza.
Mummunan harin da ‘yan bindiga suka kai ranar Juma’a a Daraga, ya yi sanadin tarwatsewar mazauna garin zuwa gudun hijira.
Rahotanni sun bayyana halin dar-dar da tashin hankali da jama’ar yankin ke ci-gaba da fuskanta tun bayan harin.
‘Yan sanda a Zamfara sun ce suna ?o?arin shawo kan matsalar tsaron da ta addabi yankin da jihar gaba ?aya.
