Tsaro: Kalaman El Rufa’i Za Su Haifar Da Matsala – Monguno

Rahotanni daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar mai ba Shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Janar Babagana Monguno ya ja kunnen Gwamnan Nasiru El-Rufai game da kalaman da ya ce gwamnan na yi kan harkokin tsaro.

Monguno ya bayyana hakan ne a yayin da yake zantawa da manema labarai a fadar shugaban kasa a karshen ganawa da shugaban kasa ya yi da hafsoshin tsaro a Abuja.

“Gwamna Nasir El-Rufai ya yi magana kan hukumomin tsaron kasar nan yana cewa wai mun san ko su wane ne ‘yan ta’addan nan, da inda suke,” a cewarsa.

Monguno ya kara da cewa “wannan shi ne babban ha?arin, musamman idan ka fara maganar da ba ta dace ba, sai kai ta fadin abin da ba shi kenan ba”.

Related posts

Leave a Comment