Labarin dake shigo mana daga Jihar Sokoto na bayyana cewar Gwamnan Jihar Aminu Waziri Tambuwal ya sha alwashin cewa ya kusa kawo karshen fitaccen ?an fashin dajin nan Bello Turji, wanda ke ci gaba da addabar jihar Sokoto duk da farautarsa da jami’an tsaro ke yi.
Gwamnan ya bayyana haka ne a ranar Asabar a wani taro da shugabannin al’umma, sa’o’i kadan bayan da wasu gungun ‘yan bindiga suka kashe wani dan kasuwa a yankin tare da yin garkuwa da mutane biyar a Kurawa da ke karamar hukumar Sabon Birnin Jihar.
‘’Dab ake da a kawo ?arshensa, kuma gwamnati ta ?auki matakan da suka kamata don yi hakan da ma kawo ?arshen yan bindigar da suka hana jama’a zaman lafiya’’ kamar yadda Premium Times ta rawaito shi yana fa?a.
