Rahotanni daga ?asar Saudiyya sun bayyana cewa a ranar Jumu’a yayin gudanar da hu?uba, wani mutumi sanye da harami yayi ?o?arin hallaka ?aya daga cikin limaman masallacin Ka’aba.
Mutumin yayi ?o?arin isa ga limamin amma sai jami’an tsaro suka farga kuma suka kama shi nan take.
Hukumar dake kula da manyan masallatai biyu masu daraja ‘Haramain Sharifain’ ita ce ta bayyana haka a shafinta na kafar sada zumunta Facebook.
Hukumar tace anyi yun?urin kashe Sheikh Baleelah a dai-dai lokacin da yake hu?ubar sallar jumu’a a masallacin ka’aba. Hakanan hukumar Haramain Sharufai ta sanya bidiyon yadda mutumin yayi ?o?arin kutsawa zuwa ga limamin da yadda jami’an tsaro suka yi gaggawar dam?e shi a shafinta na kafar sada zumunta.
A jawabin da hukumar tayi tace: “Wani mutumi ya tunkari inda mumbarin liman yake a masallacin ka’aba ri?e da makami, amma jami’an tsaro sun yi nasarar dam?e shi.”
