Ni Ba Wakilin ‘Yan Bindiga Bane – Dr.Gumi

Mashahurin Malamin addinin Islama nan mazaunin garin Kaduna Sheikh Ahmad Abubakar Mahmoud Gumi ya fito fili ya fahimtar da jama’a matsayinshi na shiga tsakanin ‘yan Bindiga da gwamnati, inda ya fayyace cewa shi ba wakilin ‘yan Bindiga bane kamar yadda wasu jama’a ke bayyanawa.

Dr. Gumi ya fa?i haka ne ya yin da tsohon Sanatan Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani ya kai masa ziyara a gidan shi dake Kaduna ranar Talata.

Shehu Sani ya kaima malamin ziyara ne domin tattauna batun akan ?alibai 39 da aka sace a makarantar koyon zamanantar da gandun daji FCFM dake Afaka, jihar Kaduna da kuma mambobin ?ungiyar addinin kirista (RCCG) takwas da aka sace kwanan nan.

Dr Ahmad Gumi yace duk wasu shirye-shirye da yakamata ayi anyi don ganin an ku?utar da ?aliban wa?anda suka ?auki tsawon makwanni biyu a hannun yan bindigan.

Ya ce akan lamarin ?aliban mun yi duk abinda yakamata, har taro muka yi da iyayen ?aliban kan suje su zauna da gwamnati.

“Na fa?awa iyayen ?aliban inda matsalar take, sunje sun zauna da gwamnati sannan suka dawo wurina. Ni ba wakilin tattaunawa da yan bindiga bane.” “A duk tattaunawar da muka yi a baya muna tabbatar da akwai wakilan gwamnati tare da mu, kafin gwamnati ta bada umarnin harbe duk wanda aka gani ?auke da bindiga.”Amma a kan ?aliban kwalejin, muna iya bakin ?o?arin mu ta hanyar tuntu?a muga ta yadda za’a warware matsalar.

Satin da ya gabata Sheikh Gumi ya shaidawa jaridar Dailytrust cewa umarnin harbi da gwamnati ta bayar ya dakatar da ?o?arinsa na ku?utar da mutanen da aka sace.

Shugaban ?asa Muhammadu Buhari ya ba jami’an tsaro umarnin harbi ga duk wanda suka gani ?auke da makami ba bisa ?a’ida ba a cikin Daji.

Related posts

Leave a Comment