Rahotanni daga Jihar Bauchi na bayyana cewar Shugaban kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP Aminu Waziri Tambuwal, ya yi zargin cewa gwamnonin da suka koma jam’iyyar APC sunyi hakan ne don kada a bincike rashawar da suka tafka a baya.
An ruwaito cewa Tambuwal ya bayyana cewa sauran gwamnonin PDP ba za su tsorata ba da dukkanin wata barazana da za’a yi musu domin su canza sheka zuwa APC.
Tambuwal, wanda ya samu wakilcin gwamnan Taraba, Darius Ishaku, ya yi magana ne a ranar Lahadi wurin taron da aka gudanar a gidan gwamnatin jihar Bauchi yayin yi wa gwamnonin Maraba zuwa jihar.
An ruwaito cewa gwamnonin sun tafi jihar Bauchi ne don yin taro kan shirin tunkarar zaben 2023 da ke tafe inda gwamna Bala Mohammed ya basu masauki a jiharsa.
Gwamnonin da suka hallarci taron sun hada da Okezie Ikpeazu (Abia); Ahmadu Fintiri (Adamawa); Udom Emmanuel, (Akwa Ibom); Douye Diri (Bayelsa); Samuel Ortom (Benue). Sauran sun hada da Ifeanyi Okowa (Delta); Godwin Obaseki (Edo); Ifeanyi Ugwuanyi (Enugu); Seyi Makinde( Oyo); Nyesom Wike( Rivers) da mataimmakin gwamnan jihar Zamfara Mahdi Aliyu.
Tambuwal ya ce PDP ce kawai za ta iyo ceto Nijeriya daga halin da ta shiga kuma za ta karbi mulkin kasa a 2023 don inganta rayuwar yan kasar. Tambuwal ya soki APC kan rashin magance matsalar tsaro Ya kuma soki gwamnatin tarayya kan gaza cin galaba kan Boko Haram cikin watanni shida kamar yadda ta yi alkawari, sai dai abubuwa kara tabarbarewa suka yi.
Gwamnan Sokoton ya ce: “Wadanda suka ce za su gama da Boko Haram cikin watanni 6, gashi yanzu shekaru 6 kuma abin sai kara tabarbarewa ya ke yi. “Yanzu muna da Boko Haram daban-daban suna adabar mu a kasar. Za mu so mu mayar da Nigeria abin da ya dace ta zama.
