Matsalar Tsaro: Lissafi Ya Kwace Wa Tinubu – Amnesty

IMG 20240226 WA0252

Kungiyar Amnesty International ta ce sace fiye da ?an gudun hijira a jihar Borno da ?alibai ?ari biyu da tamanin da bakwai da malamai a yankin Kuriga a jihar Kaduna na nuna gazawar hukumomin Najeriya na kare al’umma daga hare-haren ?an bindiga da suka kashe dubban ?an ?asar cikin shekara biyar da ta gabata.

?ungiyar, cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Juma’a ta hannun shugabanta a Najeriya, Isa Sanusi, ta bu?aci gwamnatin Najeriya ta yi duk mai yiwuwa domin ku?utar da mutanen da aka sace domin ha?a su da iyalansu.

A cewar ?ungiyar, dole ne hukumomi su gudanar da cikakken bincike mai zaman kansa kan yawaitar sace-sacen da ake yi a sassa da dama na Najeriya tare da gabatar da sakamakon binciken ga al’umma sannan su tabbatar an hukunta wa?anda aka samu da hannu a garkuwa da mutane.

Amnesty ta ce, “sace-sacen mutane da dama a baya-bayan nan ?arara sun nuna cewa shugaba Bola Tinubu da gwamnatinsa ba su da tsayayyen tsari na kawo ?arshen miyagun laifukan ?an bindiga da ke cin karensu babu babbaka a sassan jihohin Najeriya. Duk matakan tsaron da shugaba Tinubu da gwamnatinsa ke aiwatarwa ba sa tasiri,” in ji Isa Sanusi.

“Ganin yadda matsalar tsaro ke ?aruwa a Najeriya a yanzu, a bayyane take cewa batun kare rayuwa da dukiyoyin al’umma ya na ?asa cikin jerin abubuwan da gwamnati ta sa a gaba. Bai kamata a ?yale mutane su zauna cikin fargaba da tsoron hari da garkuwa ba.

Yawan gazawar hukumomin Najeriya wajen kare mutane abu ne da ba za a ta?a amincewa da shi ba kuma dole ne a kawo ?arshen sa,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Amnesty ta kuma yi kira da a tabbatar da wa?anda ke da nauyin samar da tsaro a yankunan da aka yi sace-sacen jama’a su yi bayani kan gazawar da ta jefa rayuwar ?aruruwan mutane cikin ha?ari.

A ranar Alhamis ne wasu ?an bindiga suka kai hari kan wata makarantar Firamare a Kuriga da ke jihar Kaduna inda suka sace ?alibai kimanin 287 da malaminsu guda ?aya, sai dai malamin ya samu ku?uta sai kuma ?alibi guda da ya mutu.

Related posts

Leave a Comment