Manchester City Ta Lallasa Newcastle Ci 4 Da Nema A Gasar Firimiya

Mai rike da kofin Premier League, Manchester City ta ci wasa na takwas a jere, bayan da ta doke Newcastle United 4-0 ranar Lahadi a babbar gasar Ingila.

City ta yi nasara ne a kan Newcastle United a gasar Premier League karawar mako na 18 da suka fafata a St James’ Park.

Mai jan ragamar teburin Premier ta fara cin kwallo a minti biyar da fara tamaula, bayan da mai tsaron bayan Newcastle, Ciaran Clark ya kasa hana Joao Cancelo bugo kwallon da Ruben Dias ya sa kai ta fada raga.

City ta kara na biyu a minti na 27, bayan da Cancelo ya karbi kwallo daga yadi na 35 ya kuma yanke ‘yan wasan Newcastle biyu daga nan ya buga kwallo daga wajen da’ira ta 18 ta kuma fada raga.

Riyad Mahrez ne ya zura na uku a raga mai kayatarwa kuma na 50 jumulla da ya ci a Premier League, bayan da Oleksandr Zinchenko ya bugo masa kwallon.

Daf da za a tashi daga wasan ne Raheem Sterling ya ci na hudu da ya bai wa City maki ukun da take bukata a fafatawar.

Da wannan nasarar City za ta ci gaba da jan ragamar teburi har zuwa Kirsimeti kuma karo na uku da ta yi wannan bajintar, wadda biyu daga ciki ta lashe kofin Premier League a kakar 2011-12 da kuma 2017-18.

Newcastle ta ci gaba da zama ta 19 a kasan teburi da tazarar maki uku tsakaninta da Watford wadda take ta 17 da rarar kwallaye tsakaninta da Norwich City, wadda take ta karshe kuma ta 20.

Related posts

Leave a Comment