Rahoton dake shigo mana daga Jihar Kano na bayyana cewar Asusun lamunin yara na majalisar dinkin duniya watau UNICEF ya ce kashi 70 cikin 100 na yan makarantun firamare a Najeriya basu fahimtar komai da ake koya musu a makaranta.
Masanin sadarwa na UNICEF, Mr Geoffrey Njoku, ya bayyana hakan ne ranar Juma’a a jihar Kano lokacin taron tattaunawa da manema labarai kan shirin bunkasa ilimin yara na majalisar dinkin duniya.
Ya bayyana cewar makasudin zuwan yara makaranta a farkon lokaci shine domin iya rubutu da kuma lissafi, sai dai abin damuwa shine yadda hakan ya gagara samu a mafi yawan yara.
“Tun 2010, mun yi kokarin magance matsalar yara milyan 10.5 da basu zuwa makaranta, amma duk da haka kashi 70% na yaran dake makarantar basu fahimtar darasi.”
“Ya kamata mu hada adadin kashi 70% din nan kan milyan 10.5 da basu zuwa makaranta gaba daya don a maida hankali sosai kan lamarin.”
