Tun bayan bayyanar hotunan nuna tsiraici na Jarumar Hausa Fim Rahama Sadau a kafafen sadarwa na zamani, maganganu da gutsiri tsoma suka cigaba da wakana a tsakanin jaruman Mata na kannywood na fallasa asirin juna.
Tsohuwar Jarumar masana’antar Hafsat Shehu ta fito a wani faifain bidiyo tana kuka gami da la’antar Rahama Sadau wadda ta bayyanata a matsayin Shai?aniya.
Jarumai irin su Rashida Mai Sa’a da Fati Washa suma ba a bar su a baya wajen sukar lamirin shigar ba?ala da sanannniyar jarumar ‘yan asalin garin Kaduna ta yi.
Sai dai bayan faruwar hakan ne Jaruma Mansura Isah ta bayyana a wani bidiyo tana sukar Jaruman da ke surutu akan shigar ta Rahama.
“Abin mamaki wai har da ‘yan ma?igo mazinata wurin sukar Rahama Sadau, dama ance laifi tudu ne take naka ka hango na wani”.
Da alamun kalaman Mansura Isah sun fusata wata jarumar wacce aka fi sani da Fati Slow-motion, inda ta fito ta mayar da martani ga Mansura Isa a kan fallasar da ta yi wa ‘yan matan Kannywood da suka caccaki Rahama Sadau kan shigar da tayi.
Fati ta gargadi Mansura a kan ta kiyaye ta don kada ta bari su yi tone-tone, idan ba haka ba sai ta kwance mata zani a kasuwa.
Jarumar ta wallafa a shafinta na Instagram cewa:
“Budidaddiyar wasika zuwa gareki bayarabiya ‘yar tuwo tuwo nagode Allah da nake Karya bani da aure, ai matar aure Karya tafi illar akan budurwa kuma Dan ubanki ke kinsan baki da gori akaina ko ada nina bar maki Miji kika aura amma wallah idan kika cigaba da kare masu laifi zanci ubanki na nuna maki ni mara kunyar ce ta gaske ai bansan kinyi ba sai yanzu nagani kina bata suna mace mai daraja a kannywood wadda tafiki nàsaba da tarihi mai kyau arayuwa kowa yasani @hafsatshehu48 @rashidamaisaa ita uwarkice taci uwarki arashin kunya da sanin manya ita tanada bakin da zata kare kanta, Shegiya yar dakan kuka yar maula yar ci da addini kina cinye kudin miskinan kiji tsoran Allah ki kulada da matsalar gabanki.”
