Rahotanni daga birnin tarayya Abuja na bayyana cewar Shugaban ?asa Muhammadu Buhari ya tashi daga birnin tarayya Abuja inda ya nufi birnin Landan na kasar Birtaniya a yau Lahadi.
Idan masu karatu sun tuna cewa a makon da ya gabata an shirya Shugaban kasan zai tafi Landan daga kasar Kenya bayan halartan taron majalisar dinkin duniya a Nairobi.
Rahotanni sun bayyana cewar shugaba Buhari zai ziyarci birnin na Landan ne domin duba lafiyar shi kamar yadda ya saba.
