Buratai Ya Zama Jakadan Najeriya A Jamhuriyar Benin

Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya nada tsohon shugaban hafsin sojan kasa Laftanal Janar Tukur Yusuf Buratai a matsayin jakadan Najeriya a Jamhuriyar Benin.

Kazalika shugaban ya nada tsohon babban hafsan tsaron kasar Janar Abayomi Gabriel Olonisakin mai ritaya a matsayin jakadan Kamaru.

An gabatar musu da wasikun kama aikin ne yayin wani ?an kwarya kwaryar biki da ministan harkokin wajen Najeriya Geofrey Onyeama ya jagoranta ranar Talata a Abuja

Related posts

Leave a Comment