A rahotannin da aka wallafa ranar Lahadin nan a wasu kafafen watsa labarai na jaridun Najeriya suna cewa matasa sunyi yunkurin fasa rumbun abinci na gwamnatin jihar Bauchi domin dibar ganima amma masu yun’kurin suna isa sai aka bama Shugaban ma’aikata na gidan gwamnati izinin, Dr. Ladan Salihu da ya bude masu rumbun abincin, sai suka tarar babu komai a ciki sai suka juya ba tare da sun dauki komai ba.
Mazauna wurin sunce babu wadanda sukayi yunkurin fasa rumbun abinci na gwamnati, suka kara da cewa labarin ba gaskiya bane.
Kuma a cewar jaridun sun samu wan nan labari ne a mahangar watsa labarai na zamani wato (twitter handle) na kashin kansa, shi gwamnan Jihar Bala Abdulkadir Mohammed
Ga yadda labarin ya fito a turance
“(Senator Bala A. Mohammed
Oct 25
Today, hoodlums attempted a raid on the #COVID19 palliative warehouse in Bauchi State. My Chief of Staff was informed and he ordered the warehouse to be opened. They saw it was empty, and they turned back. And that’s because we shared everything to beneficiaries as at when due.)”
Ko dajin wan nan labari, ‘Muryar Yanci’ ta nufi inda rumbunan abincin gwamnatin Jihar suke a fadar Jihar, don tabbatar da shin ko hakan ya auku ko akasin hakan, ‘Muryar Yanci’ na isa wurin sai ga Jami’an tsaro sunyi dafifi, suna jiran ko ta kwana, a daya daga cikin rumbun abinci na hanyar Jos daura da Shafa Motors,
Adamu Alhaji Sani mai gadi ne a gidan mai dab da wurin (Fillin Station) yayi karin haske kan wan nan labari cewa shi ganau ne,
“Ranar Jumma’a muna zaune da masu gadin farko sunzo munyi Sallah na Magriba, sai manyansu suka zo sauran hokomomi wai sunji abin da suka ji ya faru a Jos, maza suka kawo dauki suka zuba ma’aikata, amma ba abunda ya faru a nan hukuma suna nan a zaune, akwai masu kwana akwai masu wuni, kuma akwai kayayyaki akwai kaya da yawa a cikin nan, wanda duk yace zanga-zanga a Bauchi, saidai in na wani abu, bana kayan abinci ba”
Usman Mohammad matashi ne a gidan gona (BSADP) kuma ma zauni ne a wurin shima ya fadi cewa, “Babu gaskiya a labarin haka saboda tun shekaran jiya ina cikin anguwa babu abin da ya chanza, banda hokuman da aka kawo, babu wasu da sukazo da niyyan zasu shiga rumbun aka bude masu, gaskiya raderadi ne kawai, don wan nan babban rumbu ne, babu matasan da suka zo don su bude, saima jami’an tsaro aka karo”
Ukasha Idris mai walda ne a kusa da (BASYWOD) kuma makwabcin gidan gona (BSADP) shima ga abinda yake fadi ma ‘Muryar Yanci’ ” ni banga wasu matasan da suka tashi don suyi zanga- zanga ba, ko kuma cewa anje an bude masu wuri sunga babu, gsakiya haka baiyiwu ba”
“Jami’an tsaro suna ta yawo don tsare wan nan wuraren, domin neman zama lafiya, don kar abubuwan da ya faru a wasu wurare ya faru a nan, nidai ma zaunin gurin ne naga trela sunfi goma wadan da aka shiga dasu, har yau banji makwabci na ya samu ba, kuma nima ban samu ba”
Rabiu Kapinta shima yayi bayani a daura da Rumbun Abinci na kan hanyan zuwa yan’Tifa (garage) da zai kaika Awala daga titin bayan (Stadium)
“Gaskiya ni kam babu wanda na gani amma yau naga an turo motan polisawa a nan wajen, misalin karfe uku amma sunma tafi, bayan wannan banga wani matashi da yazo da alaman zanga-zanga ba, kuma anan nake wuni, babu wani zanga zanga karya ne kawai”
Kana ya sake cewa “akwai kayan abinci sosai, don ba a kwana biyu ba akawo kaya ba, kusan zance trela sunfi goma a cikin wuri nan na abinci, kuma na kayan tallafi ne na marayu dana korona bairos. Inji Shi.
#
Daga Adamu Shehu Bauchi
