Babban Abin Da Muka Sa Gaba Shine Inganta Rayuwar Talaka – Gwamnatin Tarayya

Rahotannin dake shigo mana daga Birnin tarayya Abuja na bayyana cewar mataimakin Shugaban ?asa, Yemi Osinbajo ya bayyana cewa gwamnatin su ta APC ta maida hankalin ta kacokan wajen inganta rayuwar al’ummar ?asar nan, musamman ma talakawa.

Osinbajo ya bayyana haka ne a lokacin da ya ke wa ?ungiyar ?wararrun Mambobin APC jawabi, lokacin da su ka kai masa ziyara a karshen makon jiya.

Osinbajo ya ce APC za ta ci gaba da tafiya a kan wannan wannan turba da ta ke a kai, ta kyautata wa al’umma, kamar yadda ta faro tun daga asali.

“Wannan jam’iyya ce ta talakawa. Kuma jam’iyya ce wadda dama ita tambarin ta shi ne ganin talaka ya amfana iyar abin da za mu iya samar masu bakin ?o?arin mu.

“Dalili ke nan mu ke da manyan tsare-tsaren bun?asa rayuwar marasa galihu da dama. Shirin SIP da wannan Gwamnantin ta ?iri?iro babu wani shiri mai ?arfin da ya kai kamar sa a Afrika. Wannan kuwa ya wadatar a gane irin muhimmancin da mu ka bai wa inganta rayuwar marasa galihu a fa?in ?asar nan.

“Jam’iyyar APC ba wai kawai jam’iyyar shiga ba ce don kawai a samu mu?aman siyasa. APC ginshi?i ce, tubali ne kuma turba ce ta inganta rayuwa da bun?asa yalwar arziki cikin al’umma.”

Da ya ke jawabi, tsohon Gwamnan Bauchi Isa Yuguda, wanda shi ne shugaban ?ungiyar, ya ce su ?wararrun da ke cikin APC sun ga ya kamata su tafi tare da Mataimakin Shugaban ?asa, a matsayin sa shi ma na ?wararre a fannin shari

Related posts

Leave a Comment